< Ezra 5 >

1 Tada su proroci Hagaj i Zaharija, sin Adonov, počeli prorokovati Judejcima u Judeji i Jeruzalemu, u ime Boga Izraelova, koji je bio nad njima;
Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
2 na to ustadoše Zerubabel, sin Šealtielov, i Ješua, sin Josadakov, i počeše zidati Dom Božji u Jeruzalemu: proroci su Božji bili s ljudima i bodrili ih.
Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
3 U to vrijeme dođoše k njima Tatnaj, satrap s onu stranu Rijeke, Šetar Boznaj i drugovi njihovi poslanici i upitaše ih: “Tko vam je dopustio da gradite ovaj hram i da podižete ove zidove?
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4 Kako se zovu ljudi koji su sagradili ovu zgradu?”
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5 Ali je oko Božje bdjelo nad starješinama judejskim, te im nisu zabranili da rade dok obavijest nije otišla Dariju i stigao o tom pismeni odgovor.
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
6 Ovo je prijepis pisma koje su kralju Dariju poslali Tatnaj, satrap s one strane Rijeke, Šetar Boznaj i njihovi drugovi poslanici s one strane Eufrata.
Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
7 Oni su mu uputili izvješće ovog sadržaja: “Kralju Dariju svaki mir!
Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
8 Neka znade kralj da smo došli u pokrajinu Judeju k Domu Boga velikoga: grade ga od krupnog kamenja, drvetom oblažu zidove; posao se brižljivo izvodi i napreduje u njihovim rukama.
Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
9 Zapitali smo njihove starješine i rekli smo im: 'Tko vam je dopustio da gradite ovaj hram i da podignete njegove zidove?'
Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
10 Pitali smo ih i za njihova imena da bismo ti javili. Tako smo i zapisali imena onih koji zapovijedaju ljudstvu.
Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
11 A oni nam ovako odgovoriše: 'Mi smo sluge Boga neba i zemlje; gradimo Hram koji je bio sagrađen prije mnogo godina i koji je bio sagradio i podigao veliki kralj Izraela.
Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
12 Ali kad su naši oci rasrdili Boga neba, on ih je predao u ruke Nabukodonozora Kaldejca, babilonskog kralja, koji je razorio ovaj Hram i odveo narod u sužanjstvo u Babilon.
Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
13 Ali prve godine Kira, kralja babilonskog, zapovjedio je kralj Kir da se ponovo sazida ovaj Dom Božji.
“Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
14 Još i zlatno i srebrno posuđe Doma Božjega, koje Nabukodonozor bijaše odnio iz svetišta u Jeruzalemu i prenio ga u svetište babilonsko, uzeo je kralj Kir iz svetišta u Babilonu i predao čovjeku po imenu Šešbasaru, koga je postavio upraviteljem,
Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
15 i rekao mu je: 'Uzmi ovo posuđe, pođi i metni ga u svetište jeruzalemsko, i neka se Dom Božji zida na svome starom mjestu.'
ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
16 Taj je Šešbasar došao, dakle, i postavio temelje Doma Božjega u Jeruzalemu. I od tada pa do danas gradi se, i još nije dovršen.'
“Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
17 Sada, dakle, ako kralj želi, neka se istraži u pismohrani kraljevoj u Babilonu je li zaista kralj Kir izdao zapovijed da se sagradi Dom Božji u Jeruzalemu. A kraljeva odluka o tome neka nam se saopći.”
Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.

< Ezra 5 >