< Jonah 2 >

1 Then Jonah prayed to the LORD, his God, out of the fish’s belly.
Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
2 He said, "I called because of my affliction to the LORD. He answered me. Out of the belly of Sheol (Sheol h7585) I cried. You heard my voice.
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
3 For you threw me into the depths, in the heart of the seas. The flood was all around me. All your waves and your billows passed over me.
Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
4 I said, ‘I have been banished from your sight; yet I will look again toward your holy temple.’
Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
5 The waters surrounded me, even to the soul. The deep was around me. The weeds were wrapped around my head.
Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
6 I went down to the bottoms of the mountains. The earth barred me in forever; yet you have brought my life up from the pit, LORD my God.
Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
7 “When my soul fainted within me, I remembered the LORD. My prayer came in to you, into your holy temple.
“Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
8 Those who regard vain idols forsake their own mercy.
“Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
9 But I will sacrifice to you with the voice of thanksgiving. I will pay that which I have vowed. Salvation belongs to the LORD.”
Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
10 Then the LORD spoke to the fish, and it vomited out Jonah on the dry land.
Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.

< Jonah 2 >