< Joshua 21 >

1 Then the heads of fathers’ houses of the Levites came near to Eleazar the priest, and to Joshua the son of Nun, and to the heads of fathers’ houses of the tribes of the children of Israel.
To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
2 They spoke to them at Shiloh in the land of Canaan, saying, “The LORD commanded through Moses to give us cities to dwell in, with their pasture lands for our livestock.”
Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
3 The children of Israel gave to the Levites out of their inheritance, according to the commandment of the LORD, these cities with their pasture lands.
Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
4 The lot came out for the families of the Kohathites. The children of Aaron the priest, who were of the Levites, had thirteen cities by lot out of the tribe of Judah, out of the tribe of the Simeonites, and out of the tribe of Benjamin.
Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
5 The rest of the children of Kohath had ten cities by lot out of the families of the tribe of Ephraim, out of the tribe of Dan, and out of the half-tribe of Manasseh.
Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
6 The children of Gershon had thirteen cities by lot out of the families of the tribe of Issachar, out of the tribe of Asher, out of the tribe of Naphtali, and out of the half-tribe of Manasseh in Bashan.
Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
7 The children of Merari according to their families had twelve cities out of the tribe of Reuben, out of the tribe of Gad, and out of the tribe of Zebulun.
Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
8 The children of Israel gave these cities with their pasture lands by lot to the Levites, as the LORD commanded by Moses.
Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
9 They gave out of the tribe of the children of Judah, and out of the tribe of the children of Simeon, these cities which are mentioned by name:
Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
10 and they were for the children of Aaron, of the families of the Kohathites, who were of the children of Levi; for theirs was the first lot.
(ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
11 They gave them Kiriath Arba, named after the father of Anak (also called Hebron), in the hill country of Judah, with its pasture lands around it.
an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
12 But they gave the fields of the city and its villages to Caleb the son of Jephunneh for his possession.
Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
13 To the children of Aaron the priest they gave Hebron with its pasture lands, the city of refuge for the man slayer, Libnah with its pasture lands,
Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
14 Jattir with its pasture lands, Eshtemoa with its pasture lands,
da Yattir, da Eshtemowa,
15 Holon with its pasture lands, Debir with its pasture lands,
da Holon, da Debir,
16 Ain with its pasture lands, Juttah with its pasture lands, and Beth Shemesh with its pasture lands: nine cities out of those two tribes.
da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
17 Out of the tribe of Benjamin, Gibeon with its pasture lands, Geba with its pasture lands,
Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
18 Anathoth with its pasture lands, and Almon with its pasture lands: four cities.
Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
19 All the cities of the children of Aaron, the priests, were thirteen cities with their pasture lands.
Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
20 The families of the children of Kohath, the Levites, even the rest of the children of Kohath, had the cities of their lot out of the tribe of Ephraim.
Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
21 They gave them Shechem with its pasture lands in the hill country of Ephraim, the city of refuge for the man slayer, and Gezer with its pasture lands,
A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
22 Kibzaim with its pasture lands, and Beth Horon with its pasture lands: four cities.
Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
23 Out of the tribe of Dan, Elteke with its pasture lands, Gibbethon with its pasture lands,
Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
24 Aijalon with its pasture lands, Gath Rimmon with its pasture lands: four cities.
Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
25 Out of the half-tribe of Manasseh, Taanach with its pasture lands, and Gath Rimmon with its pasture lands: two cities.
Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
26 All the cities of the families of the rest of the children of Kohath were ten with their pasture lands.
Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
27 They gave to the children of Gershon, of the families of the Levites, out of the half-tribe of Manasseh Golan in Bashan with its pasture lands, the city of refuge for the man slayer, and Be Eshterah with its pasture lands: two cities.
Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
28 Out of the tribe of Issachar, Kishion with its pasture lands, Daberath with its pasture lands,
daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
29 Jarmuth with its pasture lands, En Gannim with its pasture lands: four cities.
Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
30 Out of the tribe of Asher, Mishal with its pasture lands, Abdon with its pasture lands,
daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
31 Helkath with its pasture lands, and Rehob with its pasture lands: four cities.
Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
32 Out of the tribe of Naphtali, Kedesh in Galilee with its pasture lands, the city of refuge for the man slayer, Hammothdor with its pasture lands, and Kartan with its pasture lands: three cities.
daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
33 All the cities of the Gershonites according to their families were thirteen cities with their pasture lands.
Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
34 To the families of the children of Merari, the rest of the Levites, out of the tribe of Zebulun, Jokneam with its pasture lands, Kartah with its pasture lands,
Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
35 Dimnah with its pasture lands, and Nahalal with its pasture lands: four cities.
Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
36 Out of the tribe of Reuben, Bezer with its pasture lands, Jahaz with its pasture lands,
daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
37 Kedemoth with its pasture lands, and Mephaath with its pasture lands: four cities.
Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
38 Out of the tribe of Gad, Ramoth in Gilead with its pasture lands, the city of refuge for the man slayer, and Mahanaim with its pasture lands,
daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
39 Heshbon with its pasture lands, Jazer with its pasture lands: four cities in all.
Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
40 All these were the cities of the children of Merari according to their families, even the rest of the families of the Levites. Their lot was twelve cities.
Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
41 All the cities of the Levites among the possessions of the children of Israel were forty-eight cities with their pasture lands.
Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
42 Each of these cities included their pasture lands around them. It was this way with all these cities.
Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
43 So the LORD gave to Israel all the land which he swore to give to their fathers. They possessed it, and lived in it.
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
44 The LORD gave them rest all around, according to all that he swore to their fathers. Not a man of all their enemies stood before them. The LORD delivered all their enemies into their hand.
Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
45 Nothing failed of any good thing which the LORD had spoken to the house of Israel. All came to pass.
Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.

< Joshua 21 >