< Psalms 145 >

1 A praise psalm by David. I will exalt you, my God, the King. I will praise your name forever and ever.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Every day I will praise you. I will extol your name forever and ever.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 Great is the LORD, and greatly to be praised! His greatness is unsearchable.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 One generation will commend your works to another, and will declare your mighty acts.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 I will meditate on the glorious majesty of your honor, on your wondrous works.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 Men will speak of the might of your awesome acts. I will declare your greatness.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 They will utter the memory of your great goodness, and will sing of your righteousness.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 The LORD is gracious, merciful, slow to anger, and of great loving kindness.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 The LORD is good to all. His tender mercies are over all his works.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 All your works will give thanks to you, LORD. Your saints will extol you.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 They will speak of the glory of your kingdom, and talk about your power,
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 to make known to the sons of men his mighty acts, the glory of the majesty of his kingdom.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 Your kingdom is an everlasting kingdom. Your dominion endures throughout all generations. The LORD is faithful in all his words, and loving in all his deeds.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 The LORD upholds all who fall, and raises up all those who are bowed down.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 The eyes of all wait for you. You give them their food in due season.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 You open your hand, and satisfy the desire of every living thing.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 The LORD is righteous in all his ways, and gracious in all his works.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 The LORD is near to all those who call on him, to all who call on him in truth.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 He will fulfill the desire of those who fear him. He also will hear their cry, and will save them.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 The LORD preserves all those who love him, but he will destroy all the wicked.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 My mouth will speak the praise of the LORD. Let all flesh bless his holy name forever and ever.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.

< Psalms 145 >