< 1 Chronicles 19 >

1 Now it happened that Nahash, the king of the sons of Ammon, died, and his son reigned in his place.
Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 And David said: “I will act with mercy toward Hanun, the son of Nahash. For his father was gracious to me.” And so David sent messengers to console him over the death of his father. But when they had reached the land of the sons of Ammon, so that they might console Hanun,
Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
3 the leaders of the sons of Ammon said to Hanun: “Do you think that perhaps David has sent them to console you in order to honor your father? Have you not noticed that his servants came to you so that they might explore, and investigate, and examine your land?”
sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
4 And so Hanun shaved the heads and beards of the servants of David, and he cut away their tunics from the buttocks to the feet, and he sent them away.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
5 And when they had gone, and had sent word to David, (for they had suffered a great disgrace, ) he sent to meet them, and he instructed them that they should remain at Jericho until their beards grew, and then they should return.
Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
6 Then, when the sons of Ammon realized that they had committed an injury against David, both Hanun and the rest of the people sent one thousand talents of silver, so that they might hire for themselves chariots and horsemen from Mesopotamia, and from Syrian Maacah, and from Zobah.
Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
7 And they hired thirty-two thousand chariots, and the king of Maacah with his people. When these had arrived, they made camp in the region opposite Medeba. Also, the sons of Ammon, gathering from their cities, went to war.
Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
8 And when David had heard this, he sent Joab and the entire army of strong men.
Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
9 And the sons of Ammon, going out, set up a battle line before the gate of the city. But the kings who had come to their aid stood separately in the field.
Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
10 And so Joab, understanding the war to be set facing him and behind his back, chose the strongest men from all of Israel, and he went out against the Syrians.
Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
11 But the remaining portion of the people he placed under the hand of his brother Abishai. And they went out against the sons of Ammon.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
12 And he said: “If the Syrians prevail over me, then you shall be a help to me. But if the sons of Ammon prevail over you, I will be a safeguard for you.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
13 Be strengthened, and let us act manfully on behalf of our people, and on behalf of the cities of our God. And the Lord will do what is good in his own sight.”
Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
14 Therefore, Joab, and the people who were with him, went out to battle against the Syrians. And he put them to flight.
Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
15 Then the sons of Ammon, seeing that the Syrians had fled, also themselves fled from Abishai, his brother, and they entered into the city. And now Joab returned to Jerusalem.
Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
16 But the Syrians, seeing that they had fallen before Israel, sent messengers, and they brought the Syrians who were across the river. And Shophach, the leader of the military of Hadadezer, was their commander.
Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
17 When this had been reported to David, he gathered together all of Israel, and he crossed the Jordan. And he rushed toward them. And he set up a battle line facing them. And they fought against him.
Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
18 But the Syrians fled from Israel. And David killed of the Syrians seven thousand chariots, and forty thousand men on foot, and Shophach, the leader of the army.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
19 Then the servants of Hadadezer, seeing themselves to be overwhelmed by Israel, crossed over to David, and they served him. And Syria was no longer willing to offer aid to the sons of Ammon.
Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.

< 1 Chronicles 19 >