< Isaiah 53 >

1 Who has believed our report? And to whom has the arm of the Lord been revealed?
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2 And he will rise up like a tender plant in his sight, and like a root from the thirsty ground. There is no beautiful or stately appearance in him. For we looked upon him, and there was no aspect, such that we would desire him.
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3 He is despised and the least among men, a man of sorrows who knows infirmity. And his countenance was hidden and despised. Because of this, we did not esteem him.
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
4 Truly, he has taken away our weaknesses, and he himself has carried our sorrows. And we thought of him as if he were a leper, or as if he had been struck by God and humiliated.
Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
5 But he himself was wounded because of our iniquities. He was bruised because of our wickedness. The discipline of our peace was upon him. And by his wounds, we are healed.
Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
6 We have all gone astray like sheep; each one has turned aside to his own way. And the Lord has placed all our iniquity upon him.
Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
7 He was offered up, because it was his own will. And he did not open his mouth. He will be led like a sheep to the slaughter. And he will be mute like a lamb before his shearer. For he will not open his mouth.
Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
8 He was lifted up from anguish and judgment. Who will describe his life? For he has been cut off from the land of the living. Because of the wickedness of my people, I have struck him down.
Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
9 And he will be given a place with the impious for his burial, and with the rich for his death, though he has done no iniquity, nor was deceit in his mouth.
Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
10 But it was the will of the Lord to crush him with infirmity. If he lays down his life because of sin, he will see offspring with long lives, and the will of the Lord will be directed by his hand.
Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
11 Because his soul has labored, he will see and be satisfied. By his knowledge, my just servant will himself justify many, and he himself will carry their iniquities.
Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
12 Therefore, I will allot to him a great number. And he will divide the spoils of the strong. For he has handed over his life to death, and he was reputed among criminals. And he has taken away the sins of many, and he has prayed for the transgressors.
Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.

< Isaiah 53 >