< Job 31 >

1 I reached an agreement with my eyes, that I would not so much as think about a virgin.
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 For what portion should God from above hold for me, and what inheritance should the Almighty from on high keep?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Is not destruction held for the wicked and repudiation kept for those who work injustice?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Does he not examine my ways and number all my steps?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 If I have walked in vanity, or if my foot has hurried towards deceitfulness,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 let him weigh me in a just balance, and let God know my simplicity.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 If my steps have turned aside from the way, or if my heart has followed my eyes, or if a blemish has clung to my hands,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 then may I sow, and let another consume, and let my offspring be eradicated.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 If my heart has been deceived over a woman, or if I have waited in ambush at my friend’s door,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 then let my wife be the harlot of another, and let other men lean over her.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 For this is a crime and a very great injustice.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 It is a fire devouring all the way to perdition, and it roots out all that springs forth.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 If I have despised being subject to judgment with my servant or my maid, when they had any complaint against me,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 then what will I do when God rises to judge, and, when he inquires, how will I respond to him?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Is not he who created me in the womb, also he who labored to make him? And did not one and the same form me in the womb?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 If I have denied the poor what they wanted and have made the eyes of the widow wait;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 if I have eaten my morsel of food alone, while orphans have not eaten from it;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 (for from my infancy mercy grew with me, and it came out with me from my mother’s womb; )
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 if I have looked down on him who was perishing because he had no clothing and the poor without any covering,
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 if his sides have not blessed me, and if he were not warmed with the fleece of my sheep;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 if I have lifted up my hand over an orphan, even when it might seem to me that I have the advantage over him at the gate;
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 then may my shoulder fall from its joint, and may my arm, with all its bones, be broken.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 For I have always feared God, like waves flowing over me, whose weight I was unable to bear.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 If I have considered gold to be my strength, or if I have called purified gold ‘my Trust;’
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 if I have rejoiced over my great success, and over the many things my hand has obtained;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 if I gazed upon the sun when it shined and the moon advancing brightly,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 so that my heart rejoiced in secret and I kissed my hand with my mouth,
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 which is a very great iniquity and a denial against the most high God;
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 if I have been glad at the ruin of him who hated me and have exulted that evil found him,
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 for I have not been given my throat to sin by asking for a curse on his soul;
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 if the men around my tabernacle have not said: “He might give us some of his food, so that we will be filled,”
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 for the foreigner did not remain at the door, my door was open to the traveler;
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 if, as man does, I have hidden my sin and have concealed my iniquity in my bosom;
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 if I became frightened by an excessive crowd, and the disrespect of close relatives alarmed me, so that I would much rather have remained silent or have gone out the door;
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 then, would he grant me a hearing, so that the Almighty would listen to my desire, and he who judges would himself write a book,
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 which I would then carry on my shoulder and wrap around me like a crown?
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 With each of my steps, I would pronounce and offer it, as if to a prince.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 So, if my land cries out against me, and if its furrows weep with it,
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 if I have used its fruits for nothing but money and have afflicted the souls of its tillers,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 then, may thistles spring forth for me instead of grain, and thorns instead of barley. (This ended the words of Job.)
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >