< Luke 2 >

1 And it happened in those days that a decree went out from Caesar Augustus, so that the whole world would be enrolled.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 This was the first enrollment; it was made by the ruler of Syria, Quirinius.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 And all went to be declared, each one to his own city.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Then Joseph also ascended from Galilee, from the city of Nazareth, into Judea, to the city of David, which is called Bethlehem, because he was of the house and family of David,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 in order to be declared, with Mary his espoused wife, who was with child.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 Then it happened that, while they were there, the days were completed, so that she would give birth.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 And she brought forth her firstborn son. And she wrapped him in swaddling clothes and laid him in a manger, because there was no room for them at the inn.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 And there were shepherds in the same region, being vigilant and keeping watch in the night over their flock.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 And behold, an Angel of the Lord stood near them, and the brightness of God shone around them, and they were struck with a great fear.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 And the Angel said to them: “Do not be afraid. For, behold, I proclaim to you a great joy, which will be for all the people.
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 For today a Savior has been born for you in the city of David: he is Christ the Lord.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 And this will be a sign for you: you will find the infant wrapped in swaddling clothes and lying in a manger.”
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 And suddenly there was with the Angel a multitude of the celestial army, praising God and saying,
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 “Glory to God in the highest, and on earth peace to men of good will.”
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 And it happened that, when the Angels had departed from them into heaven, the shepherds said to one another, “Let us cross over to Bethlehem and see this word, which has happened, which the Lord has revealed to us.”
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 And they went quickly. And they found Mary and Joseph; and the infant was lying in a manger.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 Then, upon seeing this, they understood the word that had been spoken to them about this boy.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 And all who heard it were amazed by this, and by those things which were told to them by the shepherds.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 But Mary kept all these words, pondering them in her heart.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 And the shepherds returned, glorifying and praising God for all the things that they had heard and seen, just as it was told to them.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 And after eight days were ended, so that the boy would be circumcised, his name was called JESUS, just as he was called by the Angel before he was conceived in the womb.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 And after the days of her purification were fulfilled, according to the law of Moses, they brought him to Jerusalem, in order to present him to the Lord,
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 just as it is written in the law of the Lord, “For every male opening the womb shall be called holy to the Lord,”
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 and in order to offer a sacrifice, according to what is said in the law of the Lord, “a pair of turtledoves or two young pigeons.”
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 And behold, there was a man in Jerusalem, whose name was Simeon, and this man was just and God-fearing, awaiting the consolation of Israel. And the Holy Spirit was with him.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 And he had received an answer from the Holy Spirit: that he would not see his own death before he had seen the Christ of the Lord.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 And he went with the Spirit to the temple. And when the child Jesus was brought in by his parents, in order to act on his behalf according to the custom of the law,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 he also took him up, into his arms, and he blessed God and said:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 “Now you may dismiss your servant in peace, O Lord, according to your word.
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 For my eyes have seen your salvation,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 which you have prepared before the face of all peoples:
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 the light of revelation to the nations and the glory of your people Israel.”
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 And his father and mother were wondering over these things, which were spoken about him.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 And Simeon blessed them, and he said to his mother Mary: “Behold, this one has been set for the ruin and for the resurrection of many in Israel, and as a sign which will be contradicted.
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 And a sword will pass through your own soul, so that the thoughts of many hearts may be revealed.”
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 And there was a prophetess, Anna, a daughter of Phanuel, from the tribe of Asher. She was very advanced in years, and she had lived with her husband for seven years from her virginity.
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 And then she was a widow, even to her eighty-fourth year. And without departing from the temple, she was a servant to fasting and prayer, night and day.
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 And entering at the same hour, she confessed to the Lord. And she spoke about him to all who were awaiting the redemption of Israel.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 And after they had performed all things according to the law of the Lord, they returned to Galilee, to their city, Nazareth.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 Now the child grew, and he was strengthened with the fullness of wisdom. And the grace of God was in him.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 And his parents went every year to Jerusalem, at the time of the solemnity of Passover.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 And when he had become twelve years old, they ascended to Jerusalem, according to the custom of the feast day.
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 And having completed the days, when they returned, the boy Jesus remained in Jerusalem. And his parents did not realize this.
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 But, supposing that he was in the company, they went a day’s journey, seeking him among their relatives and acquaintances.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 And not finding him, they returned to Jerusalem, seeking him.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 And it happened that, after three days, they found him in the temple, sitting in the midst of the doctors, listening to them and questioning them.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 But all who listened to him were astonished over his prudence and his responses.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 And upon seeing him, they wondered. And his mother said to him: “Son, why have you acted this way toward us? Behold, your father and I were seeking you in sorrow.”
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 And he said to them: “How is it that you were seeking me? For did you not know that it is necessary for me to be in these things which are of my Father?”
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 And they did not understand the word that he spoke to them.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 And he descended with them and went to Nazareth. And he was subordinate to them. And his mother kept all these words in her heart.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 And Jesus advanced in wisdom, and in age, and in grace, with God and men.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.

< Luke 2 >