< 1 Chronicles 16 >

1 And they brought in the ark of God, and set it in the midst of the tent that David had spread for it; and they presented burnt-offerings and peace-offerings before God.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 And when David had ended offering up the burnt-offerings and the peace-offerings, he blessed the people in the name of Jehovah.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 And he dealt to every one of Israel, both man and woman, to every one a loaf of bread and a measure [of wine] and a raisin-cake.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 And he appointed certain of the Levites to do the service before the ark of Jehovah, and to celebrate, and to thank and praise Jehovah the God of Israel:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph the chief, and second to him Zechariah, Jeiel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah and Obed-Edom, and Jeiel, with instruments of lutes and with harps; and Asaph sounding with cymbals;
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 and Benaiah and Jahaziel the priests with trumpets continually, before the ark of the covenant of God.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Then on that day David delivered first [this psalm] to give thanks to Jehovah through Asaph and his brethren.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Give thanks unto Jehovah, call upon his name; Make known his acts among the peoples.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Sing unto him, sing psalms unto him; Meditate upon all his wondrous works.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Glory in his holy name: Let the heart of them rejoice that seek Jehovah.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Seek Jehovah and his strength, Seek his face continually;
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Remember his wondrous works which he hath done; His miracles, and the judgments of his mouth:
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 Ye seed of Israel his servant, Ye sons of Jacob, his chosen ones.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 He, Jehovah, is our God; His judgments are in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Be ye ever mindful of his covenant, The word which he commanded to a thousand generations, —
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 Which he made with Abraham, And of his oath unto Isaac;
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 And he confirmed it unto Jacob for a statute, Unto Israel for an everlasting covenant,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 Saying, Unto thee will I give the land of Canaan, The lot of your inheritance;
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 When ye were a few men in number, Of small account, and strangers in it.
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 And they went from nation to nation, And from one kingdom to another people.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 He suffered no man to oppress them, And reproved kings for their sakes,
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 [Saying, ] Touch not mine anointed ones, And do my prophets no harm.
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Sing unto Jehovah, all the earth; Publish his salvation from day to day.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Declare his glory among the nations, His wondrous works among all peoples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 For Jehovah is great, and exceedingly to be praised; And he is terrible above all gods.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 For all the gods of the peoples are idols; But Jehovah made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Majesty and splendour are before him; Strength and gladness in his place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Give unto Jehovah, ye families of peoples, Give unto Jehovah glory and strength!
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Give unto Jehovah the glory of his name! Bring an oblation, and come before him: Worship Jehovah in holy splendour.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Tremble before him, all the earth: The world also is established, it shall not be moved.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Let the heavens rejoice, and let the earth be glad; And let them say among the nations, Jehovah reigneth!
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Let the sea roar, and the fulness thereof; Let the field exult, and all that is therein.
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Then shall the trees of the forest sing out at the presence of Jehovah, For he cometh to judge the earth.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 Give thanks unto Jehovah, for he is good; For his loving-kindness [endureth] for ever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 And say, Save us, O God of our salvation, And gather us, and deliver us from the nations, To give thanks unto thy holy name, To triumph in thy praise.
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Blessed be Jehovah the God of Israel, from eternity and to eternity! And all the people said, Amen! and praised Jehovah.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 And he left there, before the ark of the covenant of Jehovah, Asaph and his brethren, to do the service before the ark continually, as every day's duty required;
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 and Obed-Edom, and their brethren, sixty-eight; Obed-Edom also, the son of Jeduthun, and Hosah as doorkeepers.
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 And Zadok the priest, and his brethren the priests, before the tabernacle of Jehovah in the high place that was at Gibeon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 to offer up burnt-offerings to Jehovah on the altar of burnt-offering continually, morning and evening, and according to all that is written in the law of Jehovah, which he commanded Israel;
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 and with them Heman and Jeduthun, and the rest that were chosen, who were expressed by name, to give thanks to Jehovah, because his loving-kindness [endureth] for ever;
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 and with them, [with] Heman and Jeduthun, trumpets and cymbals for those that should sound aloud; and the musical instruments of God. And the sons of Jeduthun were at the gate.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 And all the people departed every one to his house; and David returned to bless his household.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.

< 1 Chronicles 16 >