< Jeremiah 21 >

1 This is the message that came to Jeremiah from the Lord when King Zedekiah sent Pashhur, son of Malchijah, and the priest Zephaniah, son of Maaseiah to talk with him. They said,
Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
2 “Please speak with Lord on our behalf because Nebuchadnezzar king of Babylon is attacking us. Perhaps the Lord will do some miracle for us like all those miracles he used to do, so that Nebuchadnezzar will retreat from us.”
“Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
3 But Jeremiah replied, “Tell Zedekiah this:
Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
4 This is what the Lord, the God of Israel, says: I'm going to turn the weapons you're holding against you, the weapons you're using to fight the king of Babylon and the Babylonian army outside the wall besieging you. I'm going to bring them right into the center of this city.
‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
5 I myself will fight against you with all my power and might, with the full force of my furious anger.
Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
6 I will kill those living in this city, human beings and animals. They will die from a terrible plague.
Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
7 After that, declares the Lord, I'm going to hand you over, Zedekiah king of Judah, as well as your officers and the people who are left in this city after the plague and war and famine, to Nebuchadnezzar king of Babylon and to your enemies who want you dead. He will attack you; he won't spare you or show you any pity or mercy.
Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
8 Tell the people this as well: This is what the Lord says: Look, I'm placing before you the path of life and the path of death.
“Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
9 If you stay in this city you'll die either by sword and famine and plague, but if you leave and surrender to the Babylonians who are besieging you, you will live. In fact it will be like gaining your life as plunder from a war.
Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
10 For I am determined to bring disaster on this city, and not blessings, declares the Lord. It will be handed over to the king of Babylon, who will destroy it with fire.
Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
11 In addition tell the royal family of the king of Judah to listen to the Lord's message:
“Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
12 Descendants of David, this is what the Lord says: Make sure you judge fairly every day. Protect those who are being unjustly treated from those corrupt people, otherwise because of their evil actions my anger will blaze out like fire that can't be put out.
Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
13 Watch out, because I'm going to fight against you people who live above the valley on top of a flat rock, declares the Lord. You say, ‘Who can attack us? Who can break down our defenses?’
Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
14 I'm going to punish you as you deserve for what you've done, declares the Lord. I will set your forest on fire and it will burn up everything around you.”
Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”

< Jeremiah 21 >