< Mark 6 >

1 And he went out from there, and came into his own country; and his disciples follow him.
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 And when the sabbath day was come, he began to teach in the synagogue: and many hearing him were astonished, saying, From where has this man these things? and what wisdom is this which is given to him, that even such mighty works are worked by his hands?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Is not this the carpenter, the son of Mary, the brother of James, and Joses, and of Juda, and Simon? and are not his sisters here with us? And they were offended at him.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 But Jesus said to them, A prophet is not without honor, but in his own country, and among his own kin, and in his own house.
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 And he could there do no mighty work, save that he laid his hands on a few sick folk, and healed them.
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 And he marveled because of their unbelief. And he went round about the villages, teaching.
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 And he called to him the twelve, and began to send them forth by two and two; and gave them power over unclean spirits;
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 And commanded them that they should take nothing for their journey, save a staff only; no money, no bread, no money in their purse:
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 But be shod with sandals; and not put on two coats.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 And he said to them, In what place soever you enter into an house, there abide till you depart from that place.
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 And whoever shall not receive you, nor hear you, when you depart there, shake off the dust under your feet for a testimony against them. Truly I say to you, It shall be more tolerable for Sodom and Gomorrha in the day of judgment, than for that city.
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 And they went out, and preached that men should repent.
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 And they cast out many devils, and anointed with oil many that were sick, and healed them.
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 And king Herod heard of him; (for his name was spread abroad: ) and he said, That John the Baptist was risen from the dead, and therefore mighty works do show forth themselves in him.
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Others said, That it is Elias. And others said, That it is a prophet, or as one of the prophets.
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 But when Herod heard thereof, he said, It is John, whom I beheaded: he is risen from the dead.
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 For Herod himself had sent forth and laid hold on John, and bound him in prison for Herodias’ sake, his brother Philip’s wife: for he had married her.
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 For John had said to Herod, It is not lawful for you to have your brother’s wife.
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 Therefore Herodias had a quarrel against him, and would have killed him; but she could not:
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 For Herod feared John, knowing that he was a just man and an holy, and observed him; and when he heard him, he did many things, and heard him gladly.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 And when a convenient day was come, that Herod on his birthday made a supper to his lords, high captains, and chief estates of Galilee;
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 And when the daughter of the said Herodias came in, and danced, and pleased Herod and them that sat with him, the king said to the damsel, Ask of me whatever you will, and I will give it you.
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 And he swore to her, Whatever you shall ask of me, I will give it you, to the half of my kingdom.
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 And she went forth, and said to her mother, What shall I ask? And she said, The head of John the Baptist.
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 And she came in straightway with haste to the king, and asked, saying, I will that you give me by and by in a charger the head of John the Baptist.
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 And the king was exceeding sorry; yet for his oath’s sake, and for their sakes which sat with him, he would not reject her.
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 And immediately the king sent an executioner, and commanded his head to be brought: and he went and beheaded him in the prison,
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 And brought his head in a charger, and gave it to the damsel: and the damsel gave it to her mother.
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 And when his disciples heard of it, they came and took up his corpse, and laid it in a tomb.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 And the apostles gathered themselves together to Jesus, and told him all things, both what they had done, and what they had taught.
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 And he said to them, Come you yourselves apart into a desert place, and rest a while: for there were many coming and going, and they had no leisure so much as to eat.
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 And they departed into a desert place by ship privately.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 And the people saw them departing, and many knew him, and ran afoot thither out of all cities, and preceded them, and came together to him.
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 And Jesus, when he came out, saw much people, and was moved with compassion toward them, because they were as sheep not having a shepherd: and he began to teach them many things.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 And when the day was now far spent, his disciples came to him, and said, This is a desert place, and now the time is far passed:
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 Send them away, that they may go into the country round about, and into the villages, and buy themselves bread: for they have nothing to eat.
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 He answered and said to them, Give you them to eat. And they say to him, Shall we go and buy two hundred pennyworth of bread, and give them to eat?
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 He says to them, How many loaves have you? go and see. And when they knew, they say, Five, and two fishes.
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 And he commanded them to make all sit down by companies on the green grass.
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 And they sat down in ranks, by hundreds, and by fifties.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 And when he had taken the five loaves and the two fishes, he looked up to heaven, and blessed, and broke the loaves, and gave them to his disciples to set before them; and the two fishes divided he among them all.
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 And they did all eat, and were filled.
Dukansu suka ci suka koshi.
43 And they took up twelve baskets full of the fragments, and of the fishes.
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 And they that did eat of the loaves were about five thousand men.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 And straightway he constrained his disciples to get into the ship, and to go to the other side before to Bethsaida, while he sent away the people.
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 And when he had sent them away, he departed into a mountain to pray.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 And when even was come, the ship was in the middle of the sea, and he alone on the land.
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 And he saw them toiling in rowing; for the wind was contrary to them: and about the fourth watch of the night he comes to them, walking on the sea, and would have passed by them.
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 But when they saw him walking on the sea, they supposed it had been a spirit, and cried out:
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 For they all saw him, and were troubled. And immediately he talked with them, and says to them, Be of good cheer: it is I; be not afraid.
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 And he went up to them into the ship; and the wind ceased: and they were sore amazed in themselves beyond measure, and wondered.
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 For they considered not the miracle of the loaves: for their heart was hardened.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 And when they had passed over, they came into the land of Gennesaret, and drew to the shore.
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 And when they were come out of the ship, straightway they knew him,
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 And ran through that whole region round about, and began to carry about in beds those that were sick, where they heard he was.
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 And wherever he entered, into villages, or cities, or country, they laid the sick in the streets, and sought him that they might touch if it were but the border of his garment: and as many as touched him were made whole.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Mark 6 >