< Nehemiah 7 >

1 Now it came to pass, when the wall was built, and I had set up the doors, and the porters and the singers and the Levites were appointed,
Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
2 That I gave my brother Hanani, and Hananiah the ruler of the palace, charge over Jerusalem: for he was a faithful man, and feared God above many.
Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
3 And I said to them, Let not the gates of Jerusalem be opened until the sun be hot; and while they stand by, let them shut the doors, and bar them: and appoint watches of the inhabitants of Jerusalem, every one in his watch, and every one to be over against his house.
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
4 Now the city was large and great: but the people were few therein, and the houses were not built.
Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
5 And my God put into my heart to gather together the nobles, and the rulers, and the people, that they might be reckoned by genealogy. And I found a register of the genealogy of them which came up at the first, and found written therein,
Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
6 These are the children of the province, that went up out of the captivity, of those that had been carried away, whom Nebuchadnezzar the king of Babylon had carried away, and came again to Jerusalem and to Judah, every one to his city;
Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
7 Who came with Zerubbabel, Jeshua, Nehemiah, Azariah, Raamiah, Nahamani, Mordecai, Bilshan, Mispereth, Bigvai, Nehum, Baanah. The number, I say, of the men of the people of Israel was this;
Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
8 The children of Parosh, two thousand an hundred seventy and two.
Zuriyar Farosh mutum 2,172
9 The children of Shephatiah, three hundred seventy and two.
ta Shefatiya 372
10 The children of Arah, six hundred fifty and two.
ta Ara 652
11 The children of Pahathmoab, of the children of Jeshua and Joab, two thousand and eight hundred and eighteen.
ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
12 The children of Elam, a thousand two hundred fifty and four.
ta Elam 1,254
13 The children of Zattu, eight hundred forty and five.
ta Zattu 845
14 The children of Zaccai, seven hundred and three score.
ta Zakkai 760
15 The children of Binnui, six hundred forty and eight.
ta Binnuyi 648
16 The children of Bebai, six hundred twenty and eight.
ta Bebai 628
17 The children of Azgad, two thousand three hundred twenty and two.
ta Azgad 2,322
18 The children of Adonikam, six hundred three score and seven.
ta Adonikam 667
19 The children of Bigvai, two thousand three score and seven.
ta Bigwai 2,067
20 The children of Adin, six hundred fifty and five.
ta Adin 655
21 The children of Ater of Hezekiah, ninety and eight.
ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
22 The children of Hashum, three hundred twenty and eight.
ta Hashum 328
23 The children of Bezai, three hundred twenty and four.
ta Bezai 324
24 The children of Hariph, an hundred and twelve.
ta Harif 112
25 The children of Gibeon, ninety and five.
ta Gibeyon 95.
26 The men of Bethlehem and Netophah, an hundred fourscore and eight.
Mutanen Betlehem da na Netofa 188
27 The men of Anathoth, an hundred twenty and eight.
na Anatot 128
28 The men of Bethazmaveth, forty and two.
na Bet-Azmawet 42
29 The men of Kirjathjearim, Chephirah, and Beeroth, seven hundred forty and three.
na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
30 The men of Ramah and Gaba, six hundred twenty and one.
na Rama da na Geba 621
31 The men of Michmas, an hundred and twenty and two.
na Mikmash 122
32 The men of Bethel and Ai, an hundred twenty and three.
na Betel da na Ai 123
33 The men of the other Nebo, fifty and two.
na ɗayan Nebo 52
34 The children of the other Elam, a thousand two hundred fifty and four.
na ɗayan Elam 1,254
35 The children of Harim, three hundred and twenty.
na Harim 2 320
36 The children of Jericho, three hundred forty and five.
na Yeriko 345
37 The children of Lod, Hadid, and Ono, seven hundred twenty and one.
na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
38 The children of Senaah, three thousand nine hundred and thirty.
na Sena’a 3,930.
39 The priests: the children of Jedaiah, of the house of Jeshua, nine hundred seventy and three.
Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
40 The children of Immer, a thousand fifty and two.
ta Immer 1,052
41 The children of Pashur, a thousand two hundred forty and seven.
ta Fashhur 1,247
42 The children of Harim, a thousand and seventeen.
ta Harim 1,017.
43 The Levites: the children of Jeshua, of Kadmiel, and of the children of Hodevah, seventy and four.
Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
44 The singers: the children of Asaph, an hundred forty and eight.
Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
45 The porters: the children of Shallum, the children of Ater, the children of Talmon, the children of Akkub, the children of Hatita, the children of Shobai, an hundred thirty and eight.
Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
46 The Nethinims: the children of Ziha, the children of Hashupha, the children of Tabbaoth,
Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
47 The children of Keros, the children of Sia, the children of Padon,
da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
48 The children of Lebana, the children of Hagaba, the children of Shalmai,
da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
49 The children of Hanan, the children of Giddel, the children of Gahar,
da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
50 The children of Reaiah, the children of Rezin, the children of Nekoda,
da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
51 The children of Gazzam, the children of Uzza, the children of Phaseah,
da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
52 The children of Besai, the children of Meunim, the children of Nephishesim,
da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
53 The children of Bakbuk, the children of Hakupha, the children of Harhur,
da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
54 The children of Bazlith, the children of Mehida, the children of Harsha,
da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
55 The children of Barkos, the children of Sisera, the children of Tamah,
da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
56 The children of Neziah, the children of Hatipha.
da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
57 The children of Solomon’s servants: the children of Sotai, the children of Sophereth, the children of Perida,
Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
58 The children of Jaala, the children of Darkon, the children of Giddel,
da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
59 The children of Shephatiah, the children of Hattil, the children of Pochereth of Zebaim, the children of Amon.
Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
60 All the Nethinims, and the children of Solomon’s servants, were three hundred ninety and two.
Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
61 And these were they which went up also from Telmelah, Telharesha, Cherub, Addon, and Immer: but they could not show their father’s house, nor their seed, whether they were of Israel.
Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
62 The children of Delaiah, the children of Tobiah, the children of Nekoda, six hundred forty and two.
zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
63 And of the priests: the children of Habaiah, the children of Koz, the children of Barzillai, which took one of the daughters of Barzillai the Gileadite to wife, and was called after their name.
Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
64 These sought their register among those that were reckoned by genealogy, but it was not found: therefore were they, as polluted, put from the priesthood.
Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65 And the Tirshatha said to them, that they should not eat of the most holy things, till there stood up a priest with Urim and Thummim.
Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
66 The whole congregation together was forty and two thousand three hundred and three score,
Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
67 Beside their manservants and their maidservants, of whom there were seven thousand three hundred thirty and seven: and they had two hundred forty and five singing men and singing women.
ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
68 Their horses, seven hundred thirty and six: their mules, two hundred forty and five:
Akwai dawakai 736, alfadarai 245
69 Their camels, four hundred thirty and five: six thousand seven hundred and twenty asses.
raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
70 And some of the chief of the fathers gave to the work. The Tirshatha gave to the treasure a thousand drams of gold, fifty basins, five hundred and thirty priests’ garments.
Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
71 And some of the chief of the fathers gave to the treasure of the work twenty thousand drams of gold, and two thousand and two hundred pound of silver.
Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
72 And that which the rest of the people gave was twenty thousand drams of gold, and two thousand pound of silver, and three score and seven priests’ garments.
Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
73 So the priests, and the Levites, and the porters, and the singers, and some of the people, and the Nethinims, and all Israel, dwelled in their cities; and when the seventh month came, the children of Israel were in their cities.
Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,

< Nehemiah 7 >