< Joel 3 >

1 For, behold, in those days and at that time, when I shall have turned the captivity of Juda and Jerusalem,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 I will also gather all the Gentiles, and bring them down to the valley of Josaphat, and will plead with them there for my people and my heritage Israel, who have been dispersed among the Gentiles; and [these Gentiles] have divided my land,
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 and cast lots over my people, and have given [their] boys to harlots, and sold [their] girls for wine, and have drunk.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 And what have you to do with me, O Tyre, and Sidon, and all Galilee of the Gentiles? do you render me a recompense? or do you bear malice against me? quickly and speedily will I return your recompense on your own heads:
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 because you have taken my silver and my gold, and you have brought my choice ornaments into your temples;
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 and you have sold the children of Juda and the children of Jerusalem to the children of the Greeks, that you might expel them from their coasts.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Therefore, behold, I [will] raise them up out of the place whither you have sold them, and I will return your recompense on your own heads.
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 And I will sell your sons and your daughters into the hands of the children of Juda, and they shall sell them into captivity to a far distant nation: for the Lord has spoken [it].
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Proclaim these things among the Gentiles; declare war, arouse the warriors, draw near and go up, all you men of war.
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Beat your plowshares into swords, and your sickles into spears: let the weak say, I am strong.
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Gather yourselves together, and go in, all you nations round about, and gather yourselves there; let the timid become a warrior.
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 Let them be aroused, let all the nations go up to the valley of Josaphat: for there will I sit to judge all the Gentiles round about.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Bring forth the sickles, for the vintage is come: go in, tread [the grapes], for the press is full: cause the vats to overflow; for their wickedness is multiplied.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Noises have resounded in the valley of judgment: for the day of the Lord is near in the valley of judgment.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 The sun and the moon shall be darkened, and the stars shall withdraw their light.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 And the Lord shall cry out of Sion, and shall utter his voice from Jerusalem; and the heaven and the earth shall be shaken, but the Lord shall spare his people, and shall strengthen the children of Israel.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 And you shall know that I am the Lord your God, who dwell in Sion my holy mountain: and Jerusalem shall be holy, and strangers shall not pass through her anymore.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 And it shall come to pass in that day [that] the mountains shall drop sweet wine, and the hills shall flow with milk, and all the fountains of Juda shall flow with water, and a fountain shall go forth of the house of the Lord, and water the valley of flags.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 Egypt shall be a desolation, and Idumea shall be a desolate plain, because of the wrongs of the children of Juda, because they have shed righteous blood in their land.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 But Judea shall be inhabited for ever, and Jerusalem to all generations.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 And I will make inquisition for their blood, and will by no means leave it unavenged: and the Lord shall dwell in Sion.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Joel 3 >