< Psalms 4 >

1 For the End, a Song of David among [the ]Psalms. When I called upon [him], the God of my righteousness heard me: you have made room for me in tribulation; pity me, and listen to my prayer.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
2 O you sons of men, how long [will you be] slow of heart? therefore do you love vanity, and seek falsehood? (Pause)
Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
3 But know you that the Lord has done wondrous things for his holy one: the Lord will hear me when I cry to him.
Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
4 Be you angry, and sin not; feel compunction upon your beds for what you say in your hearts. (Pause)
Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
5 Offer the sacrifice of righteousness, and trust in the Lord.
Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
6 Many say, Who will show us good things? the light of your countenance, O Lord, has been manifested towards us.
Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
7 You have put gladness into my heart: they have been satisfied with the fruit of their corn and wine and oil.
Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
8 I will both lie down in peace and sleep: for you, Lord, only have caused me to dwell securely.
Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.

< Psalms 4 >