< Matthew 8 >

1 When he came down from the mountain, great multitudes followed him.
Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
2 Behold, a leper came to him and worshiped him, saying, “Lord, if you want to, you can make me clean.”
Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
3 Yeshua [Salvation] stretched out his hand, and touched him, saying, “I want to. Be made clean.” Immediately his tzara'at ·leprosy· was cleansed.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
4 Yeshua [Salvation] said to him, “See that you tell nobody, but go, show yourself to the priest, and offer the gift that Moses [Drawn out] commanded, as a testimony to them.”
Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
5 When he came into Capernaum [Village-Comfort, Village-Compassion], a centurion came to him, asking him,
Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
6 and saying, “Lord, my servant lies in the house paralyzed, grievously tormented.”
Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
7 Yeshua [Salvation] said to him, “I will come and heal him.”
Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
8 The centurion answered, “Lord, I’m not worthy for you to come under my roof. Just say the word, and my servant will be healed.
Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
9 For I am also a man under authority, having under myself soldiers. I tell this one, ‘Go,’ and he goes; and tell another, ‘Come,’ and he comes; and tell my servant, ‘Do this,’ and he does it.”
Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
10 When Yeshua [Salvation] heard it, he marveled, and said to those who followed, “Most certainly I tell you, I haven’t found so great a trusting faith, not even in Israel [God prevails].
Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
11 I tell you that many will come from the east and the west, and will sit down with Abraham [Father of a multitude], Isaac [Laughter], and Jacob [Supplanter] in the Kingdom of Heaven (God),
Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
12 but the children of the Kingdom will be thrown out into the outer darkness. There will be weeping and gnashing of teeth.”
Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
13 Yeshua [Salvation] said to the centurion, “Go your way. Let it be done for you as you have believed.” His servant was healed in that hour.
Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
14 When Yeshua [Salvation] came into Peter [Rock]’s house, he saw his wife’s mother lying sick with a fever.
Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
15 He touched her hand, and the fever left her. She got up and served him.
Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
16 When evening came, they brought to him many possessed with demons. He cast out the spirits with a word, and healed all who were sick;
Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
17 that it might be fulfilled which was spoken through Isaiah [Salvation of Yah] the prophet, saying, “He took our infirmities, and bore our diseases.”
Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
18 Now when Yeshua [Salvation] saw great multitudes around him, he gave the order to depart to the other side.
Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
19 A scribe came, and said to him, “Teacher, I will follow you wherever you go.”
Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
20 Yeshua [Salvation] said to him, “The foxes have holes, and the birds of the sky have nests, but the Son of Man has nowhere to lay his head.”
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
21 Another of his disciples said to him, “Lord, allow me first to go and bury my father.”
Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
22 But Yeshua [Salvation] said to him, “Follow me, and leave the dead to bury their own dead.”
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
23 When he got into a boat, his disciples followed him.
Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
24 Behold, a violent storm came up on the sea, so much that the boat was covered with the waves, but he was asleep.
Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
25 They came to him, and woke him up, saying, “Save us, Lord! We are dying!”
Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
26 He said to them, “Why are you fearful, O you of little trusting faith?” Then he got up, rebuked the wind and the sea, and there was a great calm.
Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
27 The men marveled, saying, “What kind of man is this, that even the wind and the sea obey him?”
Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
28 When he came to the other side, into the country of the Gergesenes, two people possessed by demons met him there, coming out of the tombs, exceedingly fierce, so that nobody could pass that way.
Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
29 Behold, they cried out, saying, “What do we have to do with you, Yeshua [Salvation], Ben-Elohim ·Son of Elohim God·? Have you come here to torment us before the time?”
Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
30 Now there was a herd of many pigs feeding far away from them.
Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
31 The demons begged him, saying, “If you cast us out, permit us to go away into the herd of pigs.”
Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
32 He said to them, “Go!” They came out, and went into the herd of pigs: and behold, the whole herd of pigs rushed down the cliff into the sea, and died in the water.
Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
33 Those who fed them fled, and went away into the city, and told everything, including what happened to those who were possessed with demons.
Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
34 Behold, all the city came out to meet Yeshua [Salvation]. When they saw him, they begged that he would depart from their borders.
Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.

< Matthew 8 >