< Exodus 15 >

1 Then sang Moses and the children of Israel this song unto the LORD, and spake, saying, I will sing unto the LORD, for he hath triumphed gloriously: The horse and his rider hath he thrown into the sea.
Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
2 The LORD is my strength and song, And he is become my salvation: This is my God, and I will praise him; My father’s God, and I will exalt him.
“Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
3 The LORD is a man of war: the LORD is his name.
Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
4 Pharaoh’s chariots and his host hath he cast into the sea: And his chosen captains are sunk in the Red Sea.
Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
5 The deeps cover them: They went down into the depths like a stone.
Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
6 Thy right hand, O LORD, is glorious in power, Thy right hand, O LORD, dasheth in pieces the enemy.
Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
7 And in the greatness of thine excellency thou overthrowest them that rise up against thee: Thou sendest forth thy wrath, it consumeth them as stubble.
“A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
8 And with the blast of thy nostrils the waters were piled up, The floods stood upright as an heap; The deeps were congealed in the heart of the sea.
Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
9 The enemy said, I will pursue, I will overtake, I will divide the spoil: My lust shall be satisfied upon them; I will draw my sword, my hand shall destroy them.
Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
10 Thou didst blow with thy wind, the sea covered them: They sank as lead in the mighty waters.
Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
11 Who is like unto thee, O LORD, among the gods? Who is like thee, glorious in holiness, Fearful in praises, doing wonders?
Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
12 Thou stretchedst out thy right hand, The earth swallowed them.
“Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
13 Thou in thy mercy hast led the people which thou hast redeemed: Thou hast guided them in thy strength to thy holy habitation.
A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
14 The peoples have heard, they tremble: Pangs have taken hold on the inhabitants of Philistia.
Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
15 Then were the dukes of Edom amazed; The mighty men of Moab, trembling taketh hold upon them: All the inhabitants of Canaan are melted away.
Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
16 Terror and dread falleth upon them; By the greatness of thine arm they are as still as a stone; Till thy people pass over, O LORD, Till the people pass over which thou hast purchased.
Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
17 Thou shalt bring them in, and plant them in the mountain of thine inheritance, The place, O LORD, which thou hast made for thee to dwell in, The sanctuary, O Lord, which thy hands have established.
Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
18 The LORD shall reign for ever and ever.
“Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
19 For the horses of Pharaoh went in with his chariots and with his horsemen into the sea, and the LORD brought again the waters of the sea upon them; but the children of Israel walked on dry land in the midst of the sea.
Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
20 And Miriam the prophetess, the sister of Aaron, took a timbrel in her hand; and all the women went out after her with timbrels and with dances.
Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
21 And Miriam answered them, Sing ye to the LORD, for he hath triumphed gloriously; The horse and his rider hath he thrown into the sea.
Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
22 And Moses led Israel onward from the Red Sea, and they went out into the wilderness of Shur; and they went three days in the wilderness, and found no water.
Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
23 And when they came to Marah, they could not drink of the waters of Marah, for they were bitter: therefore the name of it was called Marah.
Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
24 And the people murmured against Moses, saying, What shall we drink?
Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
25 And he cried unto the LORD; and the LORD shewed him a tree, and he cast it into the waters, and the waters were made sweet. There he made for them a statute and an ordinance, and there he proved them;
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
26 and he said, If thou wilt diligently hearken to the voice of the LORD thy God, and wilt do that which is right in his eyes, and wilt give ear to his commandments, and keep all his statutes, I will put none of the diseases upon thee, which I have put upon the Egyptians: for I am the LORD that healeth thee.
Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
27 And they came to Elim, where were twelve springs of water, and threescore and ten palm trees: and they encamped there by the waters.
Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.

< Exodus 15 >