< Isaiah 57 >

1 The righteous perisheth and no man layeth it to heart; and merciful men are taken away, none considering that the righteous is taken away from the evil [to come].
Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
2 He entereth into peace; they rest in their beds, each one that walketh in his uprightness.
Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
3 But draw near hither, ye sons of the sorceress, the seed of the adulterer and the whore.
“Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
4 Against whom do ye sport yourselves? against whom make ye a wide mouth, and draw out the tongue? are ye not children of transgression, a seed of falsehood,
Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
5 ye that inflame yourselves among the oaks, under every green tree; that slay the children in the valleys, under the clefts of the rocks?
Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
6 Among the smooth [stones] of the valley is thy portion; they, they are thy lot: even to them hast thou poured a drink offering, thou hast offered an oblation. Shall I be appeased for these things?
Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
7 Upon a high and lofty mountain hast thou set thy bed: thither also wentest thou up to offer sacrifice.
Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
8 And behind the doors and the posts hast thou set up thy memorial: for thou hast discovered [thyself] to another than me, and art gone up; thou hast enlarged thy bed, and made thee a covenant with them; thou lovedst their bed where thou sawest it.
A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
9 And thou wentest to the king with ointment, and didst increase thy perfumes, and didst send thine ambassadors far off, and didst debase thyself even unto hell. (Sheol h7585)
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol h7585)
10 Thou wast wearied with the length of thy way; yet saidst thou not, There is no hope: thou didst find a quickening of thy strength; therefore thou wast not faint.
Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
11 And of whom hast thou been afraid and in fear, that thou liest, and hast not remembered me, nor laid it to thy heart? have not I held my peace even of long time, and fearest me not?
“Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
12 I will declare thy righteousness; and as for thy works, they shall not profit thee.
Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
13 When thou criest, let them which thou hast gathered deliver thee; but the wind shall take them, a breath shall carry them all away: but he that putteth his trust in me shall possess the land, and shall inherit my holy mountain.
Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
14 And he shall say, Cast ye up, cast ye up, prepare the way, take up the stumblingblock out of the way of my people.
Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
15 For thus saith the high and lofty One that inhabiteth eternity, whose name is Holy: I dwell in the high and holy place, with him also that is of a contrite and humble spirit, to revive the spirit of the humble, and to revive the heart of the contrite ones.
Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
16 For I will not contend for ever, neither will I be always wroth: for the spirit should fail before me, and the souls which I have made.
Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
17 For the iniquity of his covetousness was I wroth and smote him, I hid [my face] and was wroth: and he went on frowardly in the way of his heart.
Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
18 I have seen his ways, and will heal him: I will lead him also, and restore comforts unto him and to his mourners.
Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
19 I create the fruit of the lips: Peace, peace, to him that is far off and to him that is near, saith the LORD; and I will heal him.
ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
20 But the wicked are like the troubled sea; for it cannot rest, and its waters cast up mire and dirt.
Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
21 There is no peace, saith my God, to the wicked.
“Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.

< Isaiah 57 >