< Jeremiah 25 >

1 The word that came to Jeremiah concerning all the people of Judah in the fourth year of Jehoiakim the son of Josiah, king of Judah; the same was the first year of Nebuchadrezzar king of Babylon;
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 the which Jeremiah the prophet spake unto all the people of Judah, and to all the inhabitants of Jerusalem, saying:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 From the thirteenth year of Josiah the son of Amon, king of Judah, even unto this day, these three and twenty years, the word of the LORD hath come unto me, and I have spoken unto you, rising up early and speaking; but ye have not hearkened.
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 And the LORD hath sent unto you all his servants the prophets, rising up early and sending them; but ye have not hearkened, nor inclined your ear to hear;
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 saying, Return ye now every one from his evil way, and from the evil of your doings, and dwell in the land that the LORD hath given unto you and to your fathers, from of old and even for evermore:
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 and go not after other gods to serve them, and to worship them, and provoke me not to anger with the work of your hands; and I will do you no hurt.
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 Yet ye have not hearkened unto me, saith the LORD; that ye might provoke me to anger with the work of your hands to your own hurt.
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 Therefore thus saith the LORD of hosts; Because ye have not heard my words,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 behold, I will send and take all the families of the north, saith the LORD, and [I will send] unto Nebuchadrezzar the king of Babylon, my servant, and will bring them against this land, and against the inhabitants thereof, and against all these nations round about; and I will utterly destroy them, and make them an astonishment, and an hissing, and perpetual desolations.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 Moreover I will take from them the voice of mirth and the voice of gladness, the voice of the bridegroom and the voice of the bride, the sound of the millstones, and the light of the candle.
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 And this whole land shall be a desolation, and an astonishment; and these nations shall serve the king of Babylon seventy years.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 And it shall come to pass, when seventy years are accomplished, that I will punish the king of Babylon, and that nation, saith the LORD, for their iniquity, and the land of the Chaldeans; and I will make it desolate for ever.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 And I will bring upon that land all my words which I have pronounced against it, even all that is written in this book, which Jeremiah hath prophesied against all the nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 For many nations and great kings shall serve themselves of them, even of them: and I will recompense them according to their deeds, and according to the work of their hands.
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 For thus saith the LORD, the God of Israel, unto me: Take the cup of the wine of this fury at my hand, and cause all the nations, to whom I send thee, to drink it.
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 And they shall drink, and reel to and fro, and be mad, because of the sword that I will send among them.
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 Then took I the cup at the LORD’S hand, and made all the nations to drink, unto whom the LORD had sent me:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 [to wit], Jerusalem, and the cities of Judah, and the kings thereof, and the princes thereof, to make them a desolation, an astonishment, an hissing, and a curse; as it is this day;
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 Pharaoh king of Egypt, and his servants, and his princes, and all his people;
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 and all the mingled people, and all the kings of the land of Uz, and all the kings of the land of the Philistines, and Ashkelon, and Gaza, and Ekron, and the remnant of Ashdod;
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 Edom, and Moab, and the children of Ammon;
Edom, Mowab da Ammon;
22 and all the kings of Tyre, and all the kings of Zidon, and the kings of the isle which is beyond the sea;
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 Dedan, and Tema, and Buz, and all that have the corners [of their hair] polled;
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 and all the kings of Arabia, and all the kings of the mingled people that dwell in the wilderness;
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 and all the kings of Zimri, and all the kings of Elam, and all the kings of the Medes;
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 and all the kings of the north, far and near, one with another; and all the kingdoms of the world, which are upon the face of the earth: and the king of Sheshach shall drink after them.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 And thou shalt say unto them, Thus saith the LORD of hosts, the God of Israel: Drink ye, and be drunken, and spue, and fall, and rise no more, because of the sword which I will send among you.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 And it shall be, if they refuse to take the cup at thine hand to drink, then shalt thou say unto them, Thus saith the LORD of hosts: Ye shall surely drink.
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 For, lo, I begin to work evil at the city which is called by my name, and should ye be utterly unpunished? Ye shall not be unpunished: for I will call for a sword upon all the inhabitants of the earth, saith the LORD of hosts.
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 Therefore prophesy thou against them all these words, and say unto them, The LORD shall roar from on high, and utter his voice from his holy habitation; he shall mightily roar against his fold; he shall give a shout, as they that tread [the grapes], against all the inhabitants of the earth.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 A noise shall come even to the end of the earth; for the LORD hath a controversy with the nations, he will plead with all flesh; as for the wicked, he will give them to the sword, saith the LORD.
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Thus saith the LORD of hosts, Behold, evil shall go forth from nation to nation, and a great tempest shall be raised up from the uttermost parts of the earth.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 And the slain of the LORD shall be at that day from one end of the earth even unto the other end of the earth: they shall not be lamented, neither gathered, nor buried; they shall be dung upon the face of the ground.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Howl, ye shepherds, and cry; and wallow yourselves [in ashes], ye principal of the flock: for the days of your slaughter are fully come, and I will break you in pieces, and ye shall fall like a pleasant vessel.
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 And the shepherds shall have no way to flee, nor the principal of the flock to escape.
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 A voice of the cry of the shepherds, and the howling of the principal of the flock! for the LORD layeth waste their pasture.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 And the peaceable folds are brought to silence because of the fierce anger of the LORD.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 He hath forsaken his covert, as the lion: for their land is become an astonishment because of the fierceness of the oppressing [sword], and because of his fierce anger.
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.

< Jeremiah 25 >