< Numbers 13 >

1 Then spake Yahweh unto Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Send for thee men and let them spy out the land of Canaan, which I am giving unto the sons of Israel, —one man each for the tribe of his fathers, shalt thou send, each one a prince among them.
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 So then Moses sent them out of the desert of Paran, at the bidding of Yahweh, —all of them, great men, heads of the sons of Israel, were they.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 And, these, are their names, —Of the tribe of Reuben, Shammua, son of Zaccur;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 Of the tribe of Simeon, Shaphat, son of Hori;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 Of the tribe of Judah, Caleb, son of Jephunneh;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 Of the tribe of Issachar, Igal, son of Joseph;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 Of the tribe of Ephraim, Hoshea, son of Nun;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 Of the tribe of Benjamin, Palti, son of Raphu;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 Of the tribe of Zebulun, Gaddiel, son of Sodi;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 Of the tribe of Joseph—of the tribe of Manasseh, Gaddi son of Susi;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 Of the tribe of Dan, Ammiel, son of Gemalli;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 Of the tribe of Asher, Sethur, son of Michael;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 Of the tribe of Naphtali, Nahbi, son of Vophsi;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 Of the tribe of Gad, Geuel, son of Machi.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 These, are the names of the men, whom Moses sent to spy out the land, —but Moses called Hoshea son of Nun, Joshua.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 So Moses sent them, to spy out the land of Canaan, —and said unto them—Go up, here in the South, Yea ye shall go up the mountain;
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 And shall see the land, what it is, —And the people that dwell thereupon, Whether they are, strong, or weak, Whether they are, few or many;
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 And what, the land, is, wherein they dwell, Whether it is, good, or, bad, —And the cities within which they dwell, Whether in camps or in strongholds;
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 And what the land is, Whether, fat, or, lean, Whether there is timber therein or is not, Then shall ye pluck up courage and take of the fruit of the land. Now the days, were the days of the first-fruits of grapes.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 So they went up, and spied out the land, —from the wilderness of Zin unto Rehob at the entering in of Hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 Yea they went up in the South and entered as far as Hebron, and there, were Ahiman Sheshai and Talmai descendants of the Anak. Now, Hebron, was built seven years, before Zoan of Egypt.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 And they entered as far as the ravine of Eschol, and cut down, from thence a branch with one cluster of grapes, and bare it on a pole between two, —also of the pomegranates and of the figs.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 That place, was called, The Ravine of Eschol ["Cluster-ravine"]—on account of the cluster, which was cut down from thence by the sons of Israel.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 And they returned from spying out the land, —at the end of forty days.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 So they took their journey, and came in unto Moses and unto Aaron and unto all the assembly of the sons of Israel into the wilderness of Paran, towards Kadesh, —and brought back word—unto them and unto all the assembly, and showed them the fruit of the land.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 And they recounted unto him, and said, We entered into the land whither thou didst send us, and surely it doth flow with milk and honey, and, this, is the fruit thereof.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 Nevertheless surely mighty, are the people that dwell in the land, —and, the cities, walled in, exceeding great, moreover also, the descendants of the Anak, saw we there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Amalek, dwelleth in the land of the South; And, the Hittite, and the Jebusite and the Amorite, dwell in the mountain And the Canaanite, dwelleth by the sea, and by the side of the Jordan.
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 And Caleb stilled the people unto Moses, —and said unto them—Let us go straight up, and possess it, for we shall, surely prevail, against it.
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 But the men who went up with him said, We cannot go up against the people, —for stronger, are they than we.
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 So they sent forth a rumour of the land which they had spied out, among the sons of Israel, saying, —As touching the land through which we passed to spy it out, it is, land that eateth up them who dwell therein, And all the people that we saw in the midst thereof, were men of great stature.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 And, there, saw we the giants, sons of Anak [descended] of the giants, —And we were in our own eyes, as grass-hoppers, And, so, were we in their eyes.
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Numbers 13 >