< Psalms 119 >

1 [ALEPH.] How happy the men of blameless life, who walk in the law of Yahweh.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 How happy they who observe his testimonies, with a whole heart, they seek him.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Yea, they have not wrought perversity, In his ways, have they walked.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Thou, hast commanded thy precepts, that they should be diligently kept.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Oh would that my ways might be settled! that I might keep thy statutes.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Then, shall I not be ashamed, when I have respect unto all thy commandments.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 I will thank thee with uprightness of heart, when I have learned thy righteous regulations.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Thy statutes, will I keep, Do not thou forsake me utterly.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 [BETH.] Wherewithal can a young man keep pure his way? By taking heed, according to thy word.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 With all my heart, have I sought thee, Suffer me not to be led astray from thy commandments.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 In my heart, have I treasured what thou hast said, to the end I may not sin against thee.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Blessed art thou, O Yahweh—Teach me thy statutes.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 With my lips, have I recounted All the regulations of thy mouth.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 In the way of thy testimonies, have I rejoiced, Like as over all riches.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 In thy precepts, will I meditate, that I may discern thy paths.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 In thy statutes, will I find my dear delight, I will not forget thy word.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 [GIMEL.] Bestow thy bounties upon thy servant—let me live, That I may observe thy word.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Unveil thou mine eyes, that I may discern Wondrous things out of thy law.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 A sojourner, am, I, in the earth, Do not hide from me, thy commandments.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 My soul is crushed with longing for thy just decisions at all times.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Thou hast rebuked the proud as accursed, who stray from thy commandments.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Roll from off me, reproach and contempt, For, thy testimonies, have I observed.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Even rulers have taken their seat, against me, have talked, Thy servant, will still meditate in thy statutes.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Yea, thy testimonies, are my dear delight, My counsellors.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 [DALETH.] My soul, cleaveth to the dust, Give me life, according to thy word.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 My ways, I recounted, and thou didst answer me, Teach me thy statutes.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 The way of thy precepts, cause thou me to understand, and I will indeed meditate in thy wonders.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 My soul weepeth itself away, for grief, Confirm thou me, according to thy word.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 The way of falsehood, take thou from me, and, with thy law, O favour me.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 The way of faithfulness, have I chosen, Thy regulations, have I deemed right.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 I have kept close to thy testimonies, O Yahweh! do not put me to shame.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 The way of thy commandments, will I run, for thou wilt enlarge my heart.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 [HE.] Point out to me, O Yahweh, the way of thy statutes, that I may observe it unto the end.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Give me understanding, that I may observe thy law, that I may keep it with a whole heart.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Guide me in the path of thy commandments, for, therein, do I find pleasure.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Incline my heart unto thy testimonies, and not unto unjust gain.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Turn away mine eyes, from beholding vanity, In thy way, give me life.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Establish, unto thy servant, thy word, which pertaineth to the reverence of thee.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Cause to pass away my reproach, that I have feared, for, thy regulations, are good.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Lo! I have longed for thy precepts, In thy righteousness, give me life.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 [WAW.] And let thy lovingkindness reach me, O Yahweh, thy salvation, according to thy word.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 So shall I have something to answer him that reproacheth me, That I have trusted in thy word.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 And do not snatch away from my mouth the word of truth in any wise, because, for thy regulation, have I waited.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 That I may keep thy law continually, to times age-abiding and beyond.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 That I may walk to and fro in a large place, because, thy precepts, have I sought.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 That I may speak of thy testimonies before kings, and not be ashamed.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 That I may find dear delight in thy commandments, which I have loved.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 That I may lift up my hands unto thy commandments, which I have loved, and may meditate in thy statutes.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 [ZAYIN.] Remember the word unto thy servant, upon which thou hast caused me to hope.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 This, is my comfort in mine affliction, that, thy word, hath given me life.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Insolent men, have derided me exceedingly, From thy law, have I not swerved.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 I have remembered thy regulations, [which have come down] from age-past times, O Yahweh, and have consoled myself.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 A raging heat, hath seized me, by reason of the lawless, who forsake thy law.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Songs, have thy statutes become to me, in my house of sojourn.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 I have remembered, in the night, thy Name, O Yahweh, and have kept thy law.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 This, have I had, because, thy precepts, have I observed.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 [HETH.] My portion, is Yahweh, I have promised that I would keep thy words.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 I have sought the smile of thy face with all my heart, Show me favour, according to thy word.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 I have thought upon my ways, and have turned my feet unto thy testimonies.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 I have hastened, and not delayed, to keep thy commandments.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 The meshes of the lawless, have surrounded me, Thy law, have I not forgotten.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 At midnight, I arise to give thanks unto thee, For thy righteous regulations.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Companion, am I, to all who revere thee, and to them who keep thy precepts.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Of thy lovingkindness, O Yahweh, the earth, is full, Thy statutes, teach thou me.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 [TETH.] Well, hast thou dealt with thy servant, O Yahweh, according to thy word.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Good judgment and knowledge, teach thou me, For, in thy commandments, have I trusted.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Before I was afflicted, I myself was going astray, but, now, thy word, have I kept.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Good, thou art, and doing good, Teach me thy statutes.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Insolent men have plastered falsehood over me, I, with a whole heart, will observe thy precepts.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Gross, like fat, is their heart, I, in thy law, have found dear delight.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 It is, well for me, that I was afflicted, That I might learn thy statutes.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Better to me, is the law of thy mouth, than thousands of gold and silver.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 [YODH.] Thine own hands, have made me, and formed me. Give me understanding, that I may learn thy commandments.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 They who revere thee, shall see me and rejoice, that, for thy word, I waited.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 I know, O Yahweh, that righteous are thy regulations, and, in faithfulness, didst thou afflict me.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Let thy lovingkindness, I beseech thee, serve to comfort me, according to thy word to thy servant.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Let thy compassions reach me, that I may live, for, thy law, is my dear delight.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Let insolent men, be ashamed, because, by means of falsehood, they have dealt with me perversely, I, will meditate in thy precepts.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Let them who revere thee, turn unto me, even they who know thy testimonies.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Let my heart be thorough in thy statutes, that I may not be ashamed.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 [KAPH.] My soul, hath languished for thy salvation, For thy word, have I hoped.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mine eyes have failed for thy word, saying, When wilt thou comfort me?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Though I have been like a wine-skin in the smoke, thy statutes, have I not forgotten.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 How few are the days of thy servant! When wilt thou execute sentence on my persecutors?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Insolent men digged for me pits, men who are not according to thy law.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 All thy commandments, are faithful, With falsehood, have they persecuted me, O help me!
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 A little more, and they had consumed me in the earth, but, I, forsake not thy precepts.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 According to thy lovingkindness, give thou me life, so will I keep the testimonies of thy mouth.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 [LAMED.] Age-abidingly, O Yahweh, hath thy word been set up in the heavens.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 To generation after generation, is thy faithfulness, Thou hast established the earth, and it standeth.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 By thy regulations, do they stand to-day, for, all, are thy servants.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Had not thy law been my dear delight, then, had I perished in mine affliction.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Unto times age-abiding, will I not forget thy precepts, For, by them, hast thou given me life.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Thine, am I, —oh save me! For, thy precepts, have I sought.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 For me, have the lawless waited, to destroy me, Thy testimonies, will I diligently consider.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 To all perfection, have I seen an end, Broad is thy commandment, exceedingly.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 [MEM.] Oh how I love thy law! All the day, is it my (meditation)
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Beyond mine enemies, will thy commandment make me wise, for, age-abidingly, shall it be mine.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Beyond all my teachers, have I shown discretion, for, thy testimonies, are my (meditation)
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Beyond the elders, will I show understanding, for, thy precepts, have I observed.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 From every way of wickedness, have I withheld my feet, that I might keep thy word.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 From thy regulations, have I not turned aside, for, thou, hast directed me.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 How smooth to my palate is thy speech, More than honey, to my mouth.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Out of thy precepts, will I get understanding, For this cause, do I hate every false way.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 [NUN.] A lamp to my feet, is thy word, and a light to my path.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 I sware, and have fulfilled, To keep thy righteous regulations.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 I have been afflicted exceedingly, —O Yahweh, give me life according to thy word.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 The freewill offerings of my mouth, accept, I pray thee, O Yahweh, And, thy regulations, teach thou me.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 My life, is in my hand continually, Yet, thy law, have I not forgotten.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 The lawless have set a snare for me, Yet, from thy precepts, have I not strayed.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 As an inheritance have I taken thy testimonies unto times age-abiding, for, the joy of my heart, they are.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 I have inclined my heart to perform thy statutes, Age-abidingly, to the end.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 [SAMECH.] Half-hearted ones, do I hate, but, thy law, do I love.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 My hiding-place and my buckler, thou art, For thy word, have I waited.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Depart from me, ye evil-doers, —that I may observe the commandments of my God.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Uphold me according to thy word, that I may live, and do not shame me out of my hope!
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Sustain me, that I may be saved, and may find dear delight in thy statutes continually.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Thou hast made light of all who stray from thy statutes, for their fraud is, falsehood.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Dross, have I accounted all the lawless of the earth, therefore do I love thy testimonies.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 My flesh, bristled up from dread of thee, and, of thy regulations, stand I in fear.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 [AYIN.] I have done justice and righteousness, —Do not leave me to mine oppressors.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Be thou surety for thy servant for good, Let not insolent men oppress me.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mine eyes, have become dim for thy salvation, and for thy righteous word.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Deal with thy servant according to thy lovingkindness, and, thy statutes, teach thou me.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Thy servant, I am—give me understanding, so shall I get to know thy testimonies.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 It is time that Yahweh should work, They have frustrated thy law!
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 For this cause, do I love thy commandments, More than gold, yea than fine gold!
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 For this cause, all thy precepts concerning all things, I deem right, Every way of falsehood, I hate.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 [PE.] Wonderful are thy testimonies, For this cause, hath my soul observed them.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 The opening of thy words, sheddeth light, Giving understanding to the simple.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 My mouth, have I opened wide, and panted, because, for thy commandments, have I longed.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Turn thyself unto me, and show me favour, —As is befitting, to the lovers of thy Name.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 My steps, direct thou by thy word, and let no iniquity, have dominion over me.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Set me free from the oppression of man, so will I keep thy precepts.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Thy face, light thou up on thy servant, and teach me thy statutes.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Streams of water, have run down mine eyes, because men have not kept thy law.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 [ZADHE.] Righteous art thou, O Yahweh, —and, equitable, are thy regulations.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Thou hast righteously commanded thy testimonies, yea in great faithfulness.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 My zeal, hath put an end to me, for mine adversaries have forgotten thy words.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Refined is thy word, to the uttermost, and, thy servant loveth it.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Small, am I, and despised, Thy precepts, have I not forgotten.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Thy righteousness, is righteous to times age-abiding, and, thy law, is truth.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Straitness and distress, have befallen me, Thy commandments, are my dear delights.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Righteous are thy testimonies, unto times age-abiding, Give me understanding, that I may live.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 [KOPH.] I have cried out with all my heart, answer me, O Yahweh; Thy statutes, will I observe.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 I have cried out unto thee, oh save me, That I may keep thy testimonies.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 I forestalled the twilight, and cried for help, For thy word, I waited.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mine eyes forestalled the night-watches, To meditate in thy word.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 My voice, O hear, according to thy lovingkindness, O Yahweh! according to thy wont, give me life.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 They have drawn near, who pursue villainy, From thy law, have they gone far away.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Near art thou, O Yahweh, and, all thy commandments, are truth.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Long, have I known, from thy testimonies, That, to times age-abiding, thou didst establish them.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 [RESH.] Behold mine affliction, and rescue me, For, thy law, have I not forgotten.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Plead my cause, and redeem me, By thy word, give me life
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Far from the lawless, is salvation, For, thy statutes, have they not sought.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Thy compassions, are great, O Yahweh, According to thy regulations, give me life.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Many, are my persecutors and mine adversaries, From thy testimonies, have I not swerved.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 I have seen traitors, and felt loathing, Because, thy word, they kept not.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 See thou that, thy precepts, I have loved, O Yahweh, according to thy lovingkindness, give me life.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 The sum of thy word, is truth, and, age-abiding, is every one of thy righteous regulations.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 [SHIN.] Rulers, have persecuted me, without cause, But, of thy word, hath my heart stood in awe.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Joyful am I over thy word, Like the finder of spoil in abundance.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Falsehood, I hate and abhor, Thy law, do I love.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Seven times in the day, have I praised thee, For thy righteous regulations.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Blessing in abundance, have the lovers of thy law, and nothing to make them stumble.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 I have looked for thy salvation, O Yahweh, and, thy commandments, have I done.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 My soul hath kept thy testimonies, yea I have loved them greatly.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 I have kept thy precepts, and thy testimonies, For, all my ways, are before thee.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 [TAU] Let my shouting come near before thee, O Yahweh, According to thy word, give me understanding.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Let my supplication come in before thee, According to thy word, deliver me.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 My lips, shall pour out, praise, When thou shalt teach me thy statutes.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 My tongue, shall respond, with thy word, For, all thy commandments, are righteous.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Be thy hand ready to help me, For, thy statutes, have I chosen.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 I have longed for thy salvation, O Yahweh, and, thy law, is my dear delight.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Let my soul live, that it may praise thee, So shall thy regulation help me.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 I have strayed like a wandering sheep, O seek thy servant, For, thy commandments, have I not forgotten.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Psalms 119 >