< Psalms 35 >

1 David’s. Contend, O Yahweh, with them who contend with me, Make war upon them who make war upon me.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Grasp buckler and shield, and arise in my help;
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Then draw the spear, and close up against my pursuers, Say to my soul, Thy salvation, I am!
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Let them be ashamed and confounded, who are seeking my life, —Let them turn back and be put to the blush, who are devising my hurt:
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Let them be as chaff before the wind, with, the messenger of Yahweh, pressing them on:
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Let their way become dark and slippery, with, the messenger of Yahweh, pursuing them.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For, without cause, have they hid for me, in a ditch, their net, —Without cause, have they digged [a pit] for my life.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 There shall reach him a ruin he could not know, —Yea, his own net which he hath hidden, shall capture him, Into that ruin, shall he fall!
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 But, my soul, shall exult in Yahweh, —shall be glad in his salvation.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 All my bones, shall say—O Yahweh, who is like unto thee? Rescuing the oppressed from one stronger than he, Yea the oppressed and the needy, from their spoiler.
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 There rise up witnesses helping forward violence and wrong, What I know not, they demand of me:
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 They repay me evil for good, Bereaving my soul.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 But, as for me, when they were sick, my clothing was sackcloth, I humbled, with fasting, my soul, though, my prayer, unto mine own bosom, might return:
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Like as for a friend, like as for a brother of mine own, I walked to and fro, As though mourning for a mother, I gloomily bowed myself down.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 But, in mine overthrow, have they rejoiced, and gathered themselves together, —There gathered themselves together against me foolish men, and I knew it not, They have torn in pieces, and not been silent;
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Amidst profane praters of perversion, have they gnashed upon me with their teeth.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 My Lord! how long wilt thou look on? Bring back my soul out of their raging, from among lions, my solitary self.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 I will thank thee, in the midst of a great convocation, —In the midst of a mighty people, will I praise thee.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Let not them who are falsely my foes rejoice over me, As for them who hate me without cause, let them not wink the eye!
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For, no salvation, will they utter, —But, against the quiet of the land, deceitful things, do they devise;
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Yea they have opened wide against me their mouth, They have said, Aha! Aha! our own eye, hath seen!
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Thou hast seen, O Yahweh, do not keep silence! O My Lord! be not far from me:
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Bestir thyself and wake up, to my vindication, O my God and My Lord!—to my plea:
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Vindicate me according to thy righteousness, O Yahweh, my God! And let them not rejoice over me:
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Let them not say in their heart, Aha! to our mind! Let them not say, We have swallowed him up!
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Let them turn pale, and then at once blush, who are rejoicing at my misfortune, —Let them be clothed with shame and confusion, who are magnifying themselves against me.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Let them shout in triumph and rejoice, who are desiring my justification; And let them say continually, Yahweh be magnified, Who hath taken pleasure in the prosperity of his servant.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 Mine own tongue also, shall softly utter thy righteousness, —All the day long, —thy praise!
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Psalms 35 >