< Romans 16 >

1 And I commend to you Phoebe our sister, —being a minister [also] of the assembly which is in Cenchreae;
Ina gabatar muku da’yar’uwarmu Fibi, baranyar ikkilisiya a Kenkireya.
2 In order that ye may give her welcome in the Lord in a manner worthy of the saints, and stand by her in any matter wherein she may have need of you; for, she also, hath proved to be a defender of many, and of my own self.
Ina roƙonku ku karɓe ta a cikin Ubangiji yadda ya dace a karɓi tsarkaka a kuma ba ta kowane irin taimakon da take bukata daga wurinku, gama ta zama mai taimako ƙwarai ga mutane masu yawa, haɗe da ni ma.
3 Salute ye Prisca and Aquila, my fellow-workers in Christ Jesus, —
Ku gai da Firiskila da Akwila, abokan aikina cikin Kiristi Yesu.
4 Who, indeed, for my life, their own neck laid down, —unto whom—not, I only, give thanks, but also all the assemblies of the nations;
Sun yi kasai da ransu saboda ni. Ba ni kaɗai nake musu godiya ba amma har ma da dukan ikkilisiyoyin Al’ummai.
5 [Salute] also the assembly at their house. Salute ye Epaenetus, my beloved, who is a first-fruit of Asia unto Christ.
Ku kuma gai da ikkilisiyar da take haɗuwa a gidansu. Ku gai da ƙaunataccen abokina Efenetus, wanda ya zama na farko a karɓar Kiristi a lardin Asiya.
6 Salute Mary—who, indeed, hath toiled much for you.
Ku gai da Maryamu wadda ta yi muku aiki tuƙuru.
7 Salute Andronicus and Junias, my kinsmen and my fellow-captives, who, indeed, are of note among the Apostles, who also before me had come to be in Christ.
Ku gai da Anduronikus da Yuniyas, dangina waɗanda aka daure a kurkuku tare da ni. Su fitattu ne sosai a cikin manzanni, sun riga ni zama masu bin Kiristi.
8 Salute Ampliatus, my beloved in the Lord.
Ku gai da Amfiliyatus, ƙaunataccena a cikin Ubangiji.
9 Salute Urbanus, our fellow-worker in Christ; and Stachys, my beloved.
Ku gai da Urbanus, abokin aikinmu cikin Kiristi, da kuma ƙaunataccen abokina Sitakis.
10 Salute Apelles, the approved in Christ. Salute them of [the household of] Aristobulus.
Ku gai da Afelles wanda amincinsa cikin Kiristi tabbatacce ne. Ku gai da iyalin gidan Aristobulus.
11 Salute Herodion, my kinsman. Salute them of [the household of] Narcissus who are in the Lord.
Ku gai da ɗan’uwana, Hirodiyon. Ku gai da iyalin gidan Narkissus da suke cikin Ubangiji.
12 Salute Tryphaena and Tryphosa, [sisters] who have toiled in the Lord. Salute Persis, the beloved [sister], who, indeed, hath toiled much in the Lord.
Ku gai da Tiryifena da Tiryifosa, matan nan da suke aiki tuƙuru cikin Ubangiji. Ku gai da ƙaunatacciyata Fersis, wata matan da ta yi aiki tuƙuru cikin Ubangiji.
13 Salute Rufus, the chosen in the Lord; also his and my mother.
Ku gai da Rufus zaɓaɓɓe cikin Ubangiji, da kuma mahaifiyarsa, wadda ta zama kamar mahaifiya a gare ni.
14 Salute Asyncritus, Phlegon, Hermes, Patrobas, Hermas, and the brethren that are with them.
Ku gai da Asinkiritus, Filegon, Hermes, Faturobas, Hermas da kuma’yan’uwan da suke tare da su.
15 Salute Philologus and Julia, Nereus and his sister, and Olympus, and all the saints that are with them.
Ku gai da Filologus, Yuliya, Nereyus da’yar’uwarsa, da kuma Olimfas da dukan tsarkakan da suke tare da su.
16 Salute ye one another, with a holy a kiss. All the assemblies of the Christ salute you.
Ku gaggai da juna da sumba mai tsarki. Dukan ikkilisiyoyin Kiristi suna gaishe ku.
17 But I beseech you, brethren, to keep an eye upon them who are causing divisions and occasions of stumbling, aside from the teaching which, ye, have learned, —and be turning away from them;
Ina roƙonku,’yan’uwa, ku yi hankali fa da masu raba tsakani, saɓanin koyarwar da kuka koya, suna sa tuntuɓe. Ku yi nesa da su.
18 For, they who are such, unto our Lord Christ are not doing service, but unto their own belly, —and, through their smooth and flattering speech, deceive the hearts of the innocent.
Gama irin waɗannan mutane ba sa bautar Ubangijinmu Kiristi, sai dai cikinsu. Ta wurin yaudara da kuma daɗin baki, suna ruɗin marasa wayo.
19 For, your obedience, unto all hath reached, —over you, therefore, I rejoice! But I wish you—to be wise, [indeed], as to that which is good, yet pure, as to that which is evil.
Kowa ya riga ya ji game da biyayyarku, don haka ina cike da farin ciki game da ku; amma ina so ku zama masu hikima game da abin da yake nagari, ku kuma zama marasa laifi ga abin da yake mugu.
20 Howbeit, the God of peace, will crush Satan under your feet shortly. The favour of our Lord Jesus, be with you.
Allah na salama zai tattake Shaiɗan ba da daɗewa ba yă kuma sa shi a ƙarƙashin sawunku. Alherin Ubangijinmu Yesu kuma yă kasance tare da ku.
21 There salute you—Timothy, my fellow-worker, and Lucius, and Jason, and Sosipater, my kinsmen.
Timoti, abokin aikina, yana gai da ku, haka ma Lusiyus, Yason, da Sosifater, dangina.
22 I, Tertius, who have written the epistle, salute you in the Lord.
Ni, Tertiyus, wanda ya rubuta wannan wasiƙa, ina gai da ku cikin Ubangiji.
23 There saluteth you—Gaius, my host and [the host] of the whole assembly. There salute you—Erastus, the steward of the city, and Quartus the brother.
Gayus, mai masauƙina, mai kuma saukar da dukan’yan Ikkilisiya, yana gaishe ku. Erastus, mai bi da ayyukan jama’ar gari, da kuma ɗan’uwanmu Kwartus, suna gaishe ku.
25 Now, unto him who hath power to establish you, according to my glad-message—even the proclamation of Jesus Christ, according to the revelation of a sacred secret, in age-past times kept silent, (aiōnios g166)
Ɗaukaka ta tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa’azin Yesu Kiristi, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil azal, (aiōnios g166)
26 But now made manifest, and through means of prophetic scriptures, according to the command of the age-abiding God, for obedience of faith unto all the nations made known, (aiōnios g166)
amma yanzu kuwa aka bayyana, aka kuma sanar ta wurin rubuce-rubucen annabawa bisa ga umarnin Allah madawwami, domin dukan al’ummai su gaskata su kuma yi masa biyayya (aiōnios g166)
27 Unto a God, wise alone, through Jesus Christ, [unto whom] be the glory, unto the ages. Amen. (aiōn g165)
ɗaukaka ta tabbata har abada ga Allah, wanda shi ne kaɗai mai hikima ta wurin Yesu Kiristi! Amin. (aiōn g165)

< Romans 16 >