< Zechariah 12 >

1 The oracle of the word of Yahweh, on Israel, —Declareth Yahweh—Stretching out the heavens, and founding the earth, and fashioning the spirit of man within him:
Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
2 Lo! I am making Jerusalem a bowl of reeling to all the peoples, round about, —Moreover also, on Judah, shall it be in the siege against Jerusalem;
“Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
3 And it shall come to pass, in that day, that I will make Jerusalem a lifting-stone, to all the peoples, all who seek to lift her, shall, cut themselves in pieces, —though all the nations of the earth, gather themselves together against her.
A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
4 In that day, Declareth Yahweh, I will smite every horse with terror, and his rider with madness, —and, over the house of Judah, will I keep opening mine eyes, and, every horse of the peoples, will I smite with blindness.
A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
5 Then will the chiefs of Judah say in their hearts, —A strength unto me, [would be] the inhabitants of Jerusalem, in Yahweh of hosts, their God.
Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
6 In that day, will I make the chiefs of Judah like a pan of fire among sticks, and like a torch of fire in a sheaf, so shall they devour, on the right hand and on the left, all the peoples round about; so shall Jerusalem yet, be inhabited, in her own place, as Jerusalem.
“A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
7 But Yahweh will save the tents of Judah first, —lest the honour of the house of David, and the honour of the inhabitant of Jerusalem, should be magnified over Judah.
“Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
8 In that day, will Yahweh, throw a covering, around the inhabitant of Jerusalem, so shall the tottering among them, in that day, become like David, —and the house of David—like God, like the messenger of Yahweh, before them.
A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
9 And it shall come to pass, in that day, —That I will seek to destroy all the nations, that come against Jerusalem.
A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
10 But I will pour out upon the house of David and upon the inhabitant of Jerusalem, the spirit of favour, and of supplications, and they will look unto me, whom they have pierced, —and will wail over him, as one waileth over an only son, and will make bitter outcry over him, as one maketh bitter outcry over a firstborn.
“Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
11 In that day, will the wailing, be great, in Jerusalem, as the wailing of Hadadrimmon, in the valley of Megiddon;
A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
12 So shall the land, wail, family by family, apart, —the family of the house of David apart, and their wives apart, the family of the house of Nathan apart, and their wives apart;
Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
13 The family of the house of Levi, apart, and their wives apart, the family of Shimei, apart, —and their wives apart:
iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
14 All the families that remain, family by family, apart, —and their wives, apart.
dukan sauran iyalan kuma da matansu.

< Zechariah 12 >