< Luke 2 >

1 And in those days it occurred, that a decree went forth from Augustus Caesar, that all the people of his dominion should be enrolled.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 And this enrollment was first made under the presidency of Quirinus in Syria.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 And everyone went to his own city to be enrolled.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 And Joseph also went up from Nazareth of Galilee to Judaea, to the city of David which is called Bethlehem, because he was of the house and lineage of David,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 with Mary his espoused, then pregnant, to be enrolled.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 And it was while they were there, that the days for her to bring forth were completed.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 And she brought forth her firstborn son, and wrapped him in bandages, and laid him in the stall; for they had no place where they could lodge.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 And there were shepherds in that region, who abode there and kept watch of their flocks by night.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 And lo, the angel of God came to them, and the glory of the Lord shone upon them: and they feared with great fear.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 And the angel said to them: Fear not; for, behold I announce to you great joy, which will be to all the world.
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 For there is born to you this day a deliverer, who is the Lord Messiah, in the city of David
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 And this is the sign for you: Ye will find the babe wrapped in bandages, and placed in a stall.
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 And instantly there were seen with the angel, the many hosts of heaven, praising God, and saying:
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 Glory to God in the highest heavens, and on earth peace and good hope for men.
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 And it was so, that when the angels had gone from them into heaven, the shepherds conferred with one another, and said: Let us go down to Bethlehem, and see this thing which hath occurred, as the Lord hath made known to us.
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 And they came hastily, and found Mary and Joseph, and the babe laid in the stall.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 And when they saw, they made known the information which was given to them concerning the child.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 And all that heard, wondered at the things that were told them by the shepherds.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 And Mary laid up all these things, and pondered them in her heart.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 And the shepherds returned glorifying and praising God for all that they had seen and heard, as it was told them.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 And when the eight days for the circumcision of the child were completed, his name was called JESUS; as he was named by the angel, before he was conceived in the womb
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 And when the days of their purification were completed, according to the law of Moses, they carried him to Jerusalem, to present him before the Lord:
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 (as it is written in the law of the Lord, that every male opening the womb shall be called holy to the Lord: )
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 and to offer a sacrifice, according as it is written in the law of the Lord, A pair of turtle-doves, or two young pigeons.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 And there was a certain man in Jerusalem, whose name was Simeon. This man was upright and just, and was waiting for the consolation of Israel, and the Holy Spirit was upon him.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 And it had been told him by the Holy Spirit, that he would not see death, until he should see the Messiah of the Lord.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 This man came, by the Spirit, into the temple; and when his parents brought in the child Jesus, to do for him as is commanded in the law,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 he took him in his arms, and blessed God, and said:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 My Lord, now release thou thy servant in peace, as thou hast said:
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 for lo, my eyes have seen thy mercy,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 which thou hast prepared in the presence of all nations,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 a light for a revelation to the Gentiles, and a glory for thy people Israel.
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 And Joseph and his mother were astonished at those things which were spoken concerning him.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 And Simeon blessed them, and said to Mary his mother: Behold, this child is set forth for the fall and for the rising of many in Israel, and for a standard of contention;
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 (and also a dart will pierce thy own soul); that the thoughts of the hearts of many may be disclosed.
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 And Hanna, a prophetess, the daughter of Phanuel, of the tribe of Asher, she also was aged in days, and, from her maidenhood, had lived seven years with her husband,
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 and was a widow of about eighty and four years, and departed not from the temple, but worshipped by day and by night with fasting and prayer;
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 and she too stood up, in that hour, and gave thanks to the Lord, and spoke of him to every one that waited for the redemption of Jerusalem.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 And when they had accomplished all things, according to the law of the Lord, they returned to Galilee, to their city Nazareth.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 And the child grew, and was strengthened in spirit, and was filled with wisdom; and the grace of God was upon him.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 And his people went up to Jerusalem every year, at the feast of the passover.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 And when he was twelve years old, they went up to the feast, as they were accustomed.
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 And when the days were completed, they returned: but the child Jesus remained at Jerusalem, and Joseph and his mother knew not of it;
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 for they supposed he was with his companions. And when they had travelled a day's journey, they sought him among their people, and inquired of every one that knew them.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 And they did not find him. And they returned again to Jerusalem, searching for him.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 And after three days, they found him in the temple, sitting in the midst of the teachers, and listening to them, and asking them questions.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 And all they that heard him, were astonished at his wisdom and his answers.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 And when they saw him they were amazed. And his mother said to him: My son, why hast thou done so to us? For lo, I and thy father have been seeking for thee with great anxiety.
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 He said to them: Why did ye seek me? Do ye not know, that it behooveth me to be in my Father's house?
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 But they did not comprehend the word that he spoke to them.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 And he went down with them, and came to Nazareth, and was obedient to them. And his mother laid up all these things in her heart.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 And Jesus increased in stature, and in wisdom, and in grace, before God and men.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.

< Luke 2 >