< Acts 3 >

1 [One day] Peter and John were going to the Temple [courtyard]. It was three o’clock in the afternoon, which was the time when people prayed [there publicly].
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 There was a man there who had been lame from the time he was born. He [was sitting by] the gate called Beautiful [Gate], at the entrance to the Temple [area]. People put him there every day, so that he could ask those who were entering [or leaving] the temple courtyard to give him some money.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 As Peter and John were about to enter [the Temple courtyard], the lame man saw them and asked them several times to give him some money. (OR, The lame man said to them several times, “Please give me some money!”)
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 As Peter and John looked directly at him, Peter said to him, “Look at us!”
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 So he looked directly at them, expecting to get some [money] from them.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 Then Peter said to him, “I do not have any money [MTY], but what I [can do], I will [do] for you. Jesus Christ, [who was] from Nazareth [town], has authorized [MTY] me [to heal you! So get up and] walk!”
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 Then Peter grasped the man’s right hand and helped him to stand up. Immediately the man’s feet and ankles became strong.
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 He jumped up and began to walk! Then he entered the Temple [area] with them, walking and leaping and praising God!
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 All the people [there] saw that man walking and praising God.
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 They recognized that he was the man who used to sit at the Beautiful Gate in the Temple [courtyard] and ask [people] for money! So all the people there were greatly amazed at what had happened to him.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 As the man clung to Peter and John, all the people were so surprised [that they did not know what to think] So they ran to the two apostles at the place [in the Temple courtyard] that is called {that [people] call} Solomon’s Porch.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 When Peter saw that, he said to the crowd, “Fellow Israelites, (you should not be surprised about what has happened to this man!/why are you so surprised about what has happened to this man?) [RHQ] And you should not stare at us, either! You seem to [RHQ] think that the two of us enabled this man to walk because we [(exc)] ourselves are powerful or because we please God very much!
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 [So I will tell you what is really happening]. Our ancestors, including Abraham, Isaac, and Jacob, worshipped God. And now he has greatly honored Jesus, who always served him. Your [leaders] brought Jesus [to the governor, Pilate], so that [his soldiers would kill him]. And [God considers that] in front of Pilate you [were the ones who rejected] Jesus [as your king], after Pilate had decided that he should release Jesus.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 [Although Jesus] always did what was right/just and good, you rejected him. [Pilate wanted to release him, but] you urgently asked Pilate to release (a murderer/someone who had killed people)!
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 [God considers that] you killed [Jesus], the one who gives people [eternal] life. But God has greatly honored him (by causing him to become alive again after he died/by raising him from the dead). Many of us saw [him after that, and now] we [(exc)] are telling [you] about it.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 It is because [we two] trusted in what Jesus [MTY, PRS] [could do, that he] made this man, whom you see and know, strong again. Yes, it is because we [(exc)] trusted in Jesus that he has completely healed this man for all of you to see.”
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 “Now, my fellow-countrymen, I know that you and your leaders did that [to Jesus] because you [and they] did not know [that he was the Messiah].
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 However, [your putting him to death] was what God had predicted that people would do. [Long ago] he told all the prophets [MTY] to write [what people would do to the Messiah. They wrote] that the Messiah, whom God [would send], would suffer [and die].
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 So, turn away from your sinful behavior and ask God [to help you] do what pleases [him], in order that he may completely forgive you for your sins.
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 [If you do that], there will be times [when you will know that] the Lord [God is] helping [you]. And some day he will [again] send back [to earth] the Messiah, whom he appointed for you. That person is Jesus.
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 Jesus must stay in heaven until the time when God will cause all that he has created to become new. Long ago God promised [to do that, and] he chose holy prophets to tell [that to people]. (aiōn g165)
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn g165)
22 For [example, the prophet] Moses said [this about the Messiah]: ‘The Lord (your God/the God whom you [worship]) will cause someone to become a prophet to tell you [God’s message. God will send him] as [he sent] me, [and he will be] from among your own people. You must listen to everything that this prophet tells you [and obey him] [SYN].
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 [Those who] do not listen to [that prophet and obey] him will no longer belong to God’s people, and [God] will get rid of them’.”
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 [Peter continued], “All the prophets have told [about what would happen during] the time [MTY] [in which we(inc) are living. Those prophets include] Samuel [and all the others who] later also spoke [about these events] before they happened.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 You [as well as we(exc)] are the people [to whom God sent the Messiah, as] the prophets said [MTY] [that he would]. And when God strongly promised [to bless] our ancestors, he also surely promised to bless you. He said to Abraham [concerning the Messiah], ‘[I] will bless all people on the earth as a result of [what] your descendant [will do].’”
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 [Peter concluded], “[So] when God sent [to the earth] (Jesus, the one who always obeys him/his servant Jesus), he sent him first to you [Israelites] to bless you. [God will] enable you to stop doing what is wicked [and to start doing what pleases him].”
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”

< Acts 3 >