< Genesis 41 >

1 Two complete years later, the king of Egypt had a dream. In the dream, he was standing alongside the Nile [River].
Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
2 Suddenly seven healthy fat cows come up out of the river. They started eating the grass that was on the riverbank.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
3 Soon seven other cows, unhealthy-looking and thin, came up behind them from the Nile [River]. They stood alongside the fat cows that were on the riverbank.
Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
4 Then the unhealthy thin cows ate the seven healthy fat cows. And then the king woke up.
Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
5 The king went to sleep again, and he had another dream. This time he saw seven heads of grain that were full of kernels of grain and ripe, and all growing on one stalk.
Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
6 After that, the king saw that seven other heads of grain sprouted on that (OR, on another) stalk. They were thin and had been dried up by the hot east wind.
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
7 Then the thin heads of grain swallowed up the seven ripe full heads. Then the king woke up. He realized that he had been dreaming.
Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
8 But the next morning he was worried about the meaning of the dream. So he summoned all the magicians and wise men who lived in Egypt. He told them what he had dreamed, but none of them could tell him the meaning of the two dreams.
Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
9 Then the chief drink-server said to the king, “Now I remember something that I should have told you! I made a mistake by forgetting to tell it to you.
Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
10 One time you were angry with two of us. So you put me and the chief baker in the prison in the house of the captain of the palace guards.
Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
11 While we were there, one night each of us had a dream, and the dreams had different meanings.
Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
12 There was a young Hebrew man there with us. He was a servant of the captain of the palace guards. We told him what we had dreamed, and he told us what our dreams meant. He told each of us the meaning of our dreams.
To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
13 And what happened was exactly the same as the meanings that he told us: You said I could have my previous job again, but the other man was killed by being hanged. [The Hebrew man’s name was Joseph].”
Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
14 When the king heard that, he told some servants to bring Joseph to him, and they quickly brought Joseph out of the prison. Joseph shaved and put on better clothes, and then he went and stood in front of the king.
Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
15 The king said to Joseph, “I had two dreams, and no one can tell me what they mean. But someone told me that when you hear someone tell about a dream he has had, you can tell that person what the dream means.”
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
16 But Joseph replied to the king, “No, I cannot do that. It is God who knows the meaning of dreams, but he will enable me to tell you their meaning, and they will mean something good.”
Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
17 The king said to Joseph, “In my first dream I was standing on the bank of the Nile [River].
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
18 Suddenly seven healthy fat cows came up out of the river, and they started eating the grass that was on the riverbank.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
19 Soon seven other cows, ugly and thin ones, came up behind them from the river. I never saw such ugly cows in all the land of Egypt!
Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
20 The thin ugly cows ate the seven fat cows that came up first.
Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
21 But afterwards, no one would have known that the thin cows ate them, because they were just as ugly as they were before. Then I woke up.
Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
22 Then I had another dream. I saw seven heads of grain. They were full of kernels of grain and ripe, and they were all growing on one stalk.
“Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
23 Then [to my surprise] I saw seven other heads of grain that sprouted. They were thin and had been dried up by the hot east wind.
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
24 The thin heads of grain swallowed the seven good heads. I told these dreams to the magicians, but none of them could explain to me what they meant.”
Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
25 Then Joseph said to the king, “Both your dreams have the same meaning. God is revealing to you in your dreams what he is about to do.
Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
26 The seven healthy cows represent seven years. The seven good heads of grain also represent seven years. The two dreams both have the same meaning.
Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
27 The seven thin ugly cows that came up behind them and the seven worthless heads of grain that were dried up by the hot east wind each represent seven years (of famine/when food will be very scarce).
Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
28 It will happen just as I have told you, because God has revealed to you what he is about to do.
“Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
29 There will be seven years in which there will be plenty of food throughout the land of Egypt,
Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
30 but after that there will be seven years (of famine/when food will be very scarce). Then people will forget all the years when there was plenty of food, because the famine that will come afterward will ruin the country.
amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
31 The people will forget how plentiful food was previously, because the famine will be very terrible.
Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
32 The reason God gave to you two dreams is that he [wants you to know] that this will happen, and he will cause it to happen very soon.
Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
33 “Now I suggest that you should choose a man who is wise and can make good decisions. I suggest that you appoint him to direct the affairs of the whole country.
“Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
34 You should also appoint supervisors over the country, in order that they can arrange to collect one-fifth of all the grain that is harvested during the seven years when food is plentiful.
Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
35 They should collect this amount of grain during those seven years that are coming, when there will be plenty of food. You should supervise them as they store it in the cities.
Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
36 This grain should be stored so that it can be eaten during the seven years when there will be a famine here in Egypt, so that the people in this country will not die from hunger.”
Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
37 The king and his officials thought that this would be a good plan.
Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
38 So the king said to them, “(Can we find any other man like Joseph, a man to whom God has given his Spirit?/It is not likely that we will find another man like this man, one to whom God has given his Spirit!)” [RHQ]
Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
39 Then the king said to Joseph, “Because God has revealed all this to you, it seems to me that there is no one who is as wise as you and who can decide wisely about things.
Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
40 So I will put you in charge of everything in my palace. All the people here in Egypt must obey what you command. Only because I am king [MTY] will I have more authority than you.”
Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
41 Then the king said to Joseph, “I am now putting you in charge of the whole country of Egypt.”
Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
42 The king took from his finger the ring that had his seal on it, and he put it on Joseph’s finger. He put robes made of fine linen on him, and he put a gold chain around his neck.
Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
43 Then he arranged for Joseph to ride around in the chariot [that showed that he was] the second-most important man in the country. When Joseph rode in the chariot, men shouted to the people who were on the road in front of him, “Get off the road!” So the king put Joseph in charge of everything in the country.
Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
44 The king said to Joseph, “I am the king, but no one in the whole land of Egypt will do anything [IDM] if you do not permit them to do it.”
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
45 The king gave Joseph a new name, Zaphenath-Paneah. He also gave him Asenath to be his wife. She was the daughter of Potiphera, who was a priest in a temple in On [city]. Then Joseph became known (OR, traveled) through all the land of Egypt.
Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
46 Joseph was 30 years old when he started to work for the king of Egypt. To do his work, he left the king’s palace and traveled throughout Egypt.
Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
47 During the next seven years, the land produced abundant crops, so there was plenty of food.
A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
48 As Joseph supervised them, his helpers collected one-fifth of all the grain that was produced during those years, and stored it in the cities. In each city, he had his helpers store up the grain that was grown in the fields that surrounded that city.
Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
49 Joseph had them store up a huge amount of grain. It looked as plentiful as the sand on the seashore. There was so much grain that after a while they stopped keeping records of how much grain was stored, because there was more grain than they could measure.
Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
50 Before the seven years of famine started, Joseph’s wife Asenath gave birth to two sons.
Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
51 Joseph named the first one Manasseh, [which sounds like the Hebrew word that means ‘forget]’, because, he said, “God has caused me to forget all my troubles and all my father’s family.”
Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
52 He named his second son Ephraim, [which means ‘to have children]’, because, he said, “God has given me children here in this land where I have suffered.”
Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
53 Finally the seven years in which there was plenty of food ended.
Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
54 Then the seven years of famine started, just as Joseph had predicted. There was also a famine in all the other nearby lands, but although the crops did not grow, there was food everywhere in Egypt, because of the grain they had stored up in the cities.
sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
55 When all the people of [MTY] Egypt had eaten all of their own food and were still hungry, they begged the king for food. So the king told all the people of Egypt, “Go to Joseph, and do what he tells you to do.”
Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
56 When the famine was very bad throughout the whole country, Joseph ordered his helpers to open the storehouses. Then they sold the grain in the storehouses to the people of Egypt, because the famine was very severe all over Egypt.
Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
57 And people from many [HYP] nearby countries came to Egypt to buy grain from Joseph, because the famine was very severe everywhere [HYP].
Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.

< Genesis 41 >