< Job 37 >

1 At this also my heart trembleth, and is moved out of its place.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Hear attentively the noise of his voice, and the sound that goeth out of his mouth.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 He directeth it under the whole heaven, and his lightning to the ends of the earth.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 After it a voice roareth: he thundereth with the voice of his excellency; and he will not restrain them when his voice is heard.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 God thundereth marvellously with his voice; great things he doeth, which we cannot comprehend.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 For he saith to the snow, Be thou on the earth; likewise to the small rain, and to the great rain of his strength.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 He sealeth up the hand of every man; that all men may know his work.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Then the beasts go into dens, and remain in their places.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 From the south cometh the whirlwind: and cold from the north.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 By the breath of God frost is given: and the breadth of the waters is narrowed.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Also by watering he wearieth the thick cloud: he scattereth his bright cloud:
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 And it is turned around by his counsels: that they may do whatever he commandeth them upon the face of the world on the earth.
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 He causeth it to come, whether for correction, or for his land, or for mercy.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Hearken to this, O Job: stand still, and consider the wondrous works of God.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Dost thou know when God disposed them, and caused the light of his cloud to shine?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Dost thou know the balancings of the clouds, the wondrous works of him who is perfect in knowledge?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 How thy garments are warm, when he quieteth the earth by the south wind?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Hast thou with him spread out the sky, which is strong, and as a molten looking glass?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Teach us what we shall say to him; for we cannot order our speech by reason of darkness.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Shall it be told him that I speak? if a man shall speak, surely he shall be swallowed up.
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 And now men see not the bright light which is in the clouds: but the wind passeth, and cleanseth them.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Fair weather cometh from the north: with God is terrible majesty.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 As for the Almighty, we cannot find him out: he is excellent in power, and in judgment, and in abundance of justice: he will not afflict.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Men therefore fear him: he respecteth not any that are wise of heart.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Job 37 >