< 2 Kings 21 >

1 Manasseh [was] twelve years old when he began to reign, and he reigned fifty and five years in Jerusalem. And his mother's name [was] Hephzi-bah.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 And he did [that which was] evil in the sight of the LORD, after the abominations of the heathen, whom the LORD cast out before the children of Israel.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 For he built again the high places which Hezekiah his father had destroyed; and he reared altars for Baal, and made a grove, as did Ahab king of Israel; and worshiped all the host of heaven, and served them.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 And he built altars in the house of the LORD, of which the LORD said, In Jerusalem will I put my name.
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 And he built altars for all the host of heaven in the two courts of the house of the LORD.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 And he made his son pass through the fire, and observed times, and used enchantments, and dealt with familiar spirits and wizards: he committed much wickedness in the sight of the LORD, to provoke [him] to anger.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 And he set a graven image of the grove that he had made in the house, of which the LORD said to David, and to Solomon his son, In this house, and in Jerusalem, which I have chosen out of all tribes of Israel, will I put my name for ever:
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Neither will I make the feet of Israel move any more out of the land which I gave their fathers; only if they will observe to do according to all that I have commanded them, and according to all the law that my servant Moses commanded them.
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 But they hearkened not: and Manasseh seduced them to do more evil than did the nations whom the LORD destroyed before the children of Israel.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 And the LORD spoke by his servants the prophets, saying,
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 Because Manasseh king of Judah hath done these abominations, [and] hath done wickedly above all that the Amorites did, who [were] before him, and hath made Judah also to sin with his idols:
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 Therefore thus saith the LORD God of Israel, Behold, I [am] bringing [such] evil upon Jerusalem and Judah, that whoever heareth of it, both his ears shall tingle.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 And I will stretch over Jerusalem the line of Samaria, and the plummet of the house of Ahab: and I will wipe Jerusalem as [a man] wipeth a dish, wiping [it], and turning [it] upside down.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 And I will forsake the remnant of my inheritance, and deliver them into the hand of their enemies; and they shall become a prey and a spoil to all their enemies;
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 Because they have done [that which was] evil in my sight, and have provoked me to anger, since the day their fathers came out of Egypt, even to this day.
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Moreover, Manasseh shed innocent blood very much, till he had filled Jerusalem from one end to another; besides his sin with which he made Judah to sin, in doing evil in the sight of the LORD.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Now the rest of the acts of Manasseh, and all that he did, and his sin that he sinned, [are] they not written in the book of the chronicles of the kings of Judah?
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 And Manasseh slept with his fathers, and was buried in the garden of his own house, in the garden of Uzza: and Amon his son reigned in his stead.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 Amon [was] twenty and two years old when he began to reign, and he reigned two years in Jerusalem. And his mother's name [was] Meshullemeth, the daughter of Haruz of Jotbah.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 And he did [that which was] evil in the sight of the LORD, as his father Manasseh did.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 And he walked in all the way that his father walked in, and served the idols that his father served, and worshiped them:
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 And he forsook the LORD God of his fathers, and walked not in the way of the LORD.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 And the servants of Amon conspired against him, and slew the king in his own house.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 And the people of the land slew all them that had conspired against king Amon; and the people of the land made Josiah his son king in his stead.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Now the rest of the acts of Amon which he did, [are] they not written in the book of the chronicles of the kings of Judah?
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
26 And he was buried in his sepulcher in the garden of Uzza: and Josiah his son reigned in his stead.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kings 21 >