< Psalms 31 >

1 For the Chief Musician. A Psalm by David. In you, LORD, I take refuge. Let me never be disappointed. Deliver me in your righteousness.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
2 Bow down your ear to me. Deliver me speedily. Be to me a strong rock, a house of defence to save me.
Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 For you are my rock and my fortress, therefore for your name’s sake lead me and guide me.
Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 Pluck me out of the net that they have laid secretly for me, for you are my stronghold.
Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
5 Into your hand I commend my spirit. You redeem me, LORD, God of truth.
Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
6 I hate those who regard lying vanities, but I trust in the LORD.
Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
7 I will be glad and rejoice in your loving kindness, for you have seen my affliction. You have known my soul in adversities.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
8 You have not shut me up into the hand of the enemy. You have set my feet in a large place.
Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
9 Have mercy on me, LORD, for I am in distress. My eye, my soul, and my body waste away with grief.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
10 For my life is spent with sorrow, my years with sighing. My strength fails because of my iniquity. My bones are wasted away.
Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
11 Because of all my adversaries I have become utterly contemptible to my neighbours, a horror to my acquaintances. Those who saw me on the street fled from me.
Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
12 I am forgotten from their hearts like a dead man. I am like broken pottery.
An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
13 For I have heard the slander of many, terror on every side, while they conspire together against me, they plot to take away my life.
Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
14 But I trust in you, LORD. I said, “You are my God.”
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15 My times are in your hand. Deliver me from the hand of my enemies, and from those who persecute me.
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16 Make your face to shine on your servant. Save me in your loving kindness.
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17 Let me not be disappointed, LORD, for I have called on you. Let the wicked be disappointed. Let them be silent in Sheol. (Sheol h7585)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
18 Let the lying lips be mute, which speak against the righteous insolently, with pride and contempt.
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
19 Oh how great is your goodness, which you have laid up for those who fear you, which you have worked for those who take refuge in you, before the sons of men!
Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
20 In the shelter of your presence you will hide them from the plotting of man. You will keep them secretly in a dwelling away from the strife of tongues.
Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
21 Praise be to the LORD, for he has shown me his marvellous loving kindness in a strong city.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
22 As for me, I said in my haste, “I am cut off from before your eyes.” Nevertheless you heard the voice of my petitions when I cried to you.
Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
23 Oh love the LORD, all you his saints! The LORD preserves the faithful, and fully recompenses him who behaves arrogantly.
Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
24 Be strong, and let your heart take courage, all you who hope in the LORD.
Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.

< Psalms 31 >