< Job 9 >

1 Then Job answered,
Sai Ayuba ya amsa,
2 “Truly I know that it is so, but how can man be just with God?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 If he is pleased to contend with him, he can’t answer him one time in a thousand.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 God is wise in heart, and mighty in strength. Who has hardened himself against him and prospered?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 He removes the mountains, and they don’t know it, when he overturns them in his anger.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 He shakes the earth out of its place. Its pillars tremble.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 He commands the sun and it doesn’t rise, and seals up the stars.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 He alone stretches out the heavens, and treads on the waves of the sea.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 He makes the Bear, Orion, and the Pleiades, and the rooms of the south.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 He does great things past finding out; yes, marvelous things without number.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Behold, he goes by me, and I don’t see him. He passes on also, but I don’t perceive him.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Behold, he snatches away. Who can hinder him? Who will ask him, ‘What are you doing?’
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 “God will not withdraw his anger. The helpers of Rahab stoop under him.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 How much less will I answer him, and choose my words to argue with him?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Though I were righteous, yet I wouldn’t answer him. I would make supplication to my judge.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 If I had called, and he had answered me, yet I wouldn’t believe that he listened to my voice.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 For he breaks me with a storm, and multiplies my wounds without cause.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 He will not allow me to catch my breath, but fills me with bitterness.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 If it is a matter of strength, behold, he is mighty! If of justice, ‘Who,’ says he, ‘will summon me?’
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Though I am righteous, my own mouth will condemn me. Though I am blameless, it will prove me perverse.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 I am blameless. I don’t respect myself. I despise my life.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 “It is all the same. Therefore I say he destroys the blameless and the wicked.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 If the scourge kills suddenly, he will mock at the trial of the innocent.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 The earth is given into the hand of the wicked. He covers the faces of its judges. If not he, then who is it?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 “Now my days are swifter than a runner. They flee away. They see no good.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 They have passed away as the swift ships, as the eagle that swoops on the prey.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 If I say, ‘I will forget my complaint, I will put off my sad face, and cheer up,’
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 I am afraid of all my sorrows. I know that you will not hold me innocent.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 I will be condemned. Why then do I labor in vain?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 If I wash myself with snow, and cleanse my hands with lye,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 yet you will plunge me in the ditch. My own clothes will abhor me.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 For he is not a man, as I am, that I should answer him, that we should come together in judgment.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 There is no umpire between us, that might lay his hand on us both.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Let him take his rod away from me. Let his terror not make me afraid;
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 then I would speak, and not fear him, for I am not so in myself.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >