< 1 Samuel 15 >

1 And Samuel saith unto Saul, 'Me did Jehovah send to anoint thee for king over His people, over Israel; and now, hearken to the voice of the words of Jehovah:
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
2 'Thus said Jehovah of Hosts, I have looked after that which Amalek did to Israel, that which he laid for him in the way in his going up out of Egypt.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
3 Now, go, and thou hast smitten Amalek, and devoted all that it hath, and thou hast no pity on it, and hast put to death from man unto woman, from infant unto suckling, from ox unto sheep, from camel unto ass.'
Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
4 And Saul summoneth the people, and inspecteth them in Telaim, two hundred thousand footmen, and ten thousand [are] men of Judah.
Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
5 And Saul cometh in unto a city of Amalek, and layeth wait in a valley;
Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
6 and Saul saith unto the Kenite, 'Go, turn aside, go down from the midst of Amalek, lest I consume thee with it, and thou didst kindness with all the sons of Israel, in their going up out of Egypt;' and the Kenite turneth aside from the midst of Amalek.
Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
7 And Saul smiteth Amalek from Havilah — thy going in to Shur, which [is] on the front of Egypt,
Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
8 and he catcheth Agag king of Amalek alive, and all the people he hath devoted by the mouth of the sword;
Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
9 and Saul hath pity — also the people — on Agag, and on the best of the flock, and of the herd, and of the seconds, and on the lambs, and on all that [is] good, and have not been willing to devote them; and all the work, despised and wasted — it they devoted.
Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
10 And the word of Jehovah is unto Samuel, saying,
Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
11 'I have repented that I caused Saul to reign for king, for he hath turned back from after Me, and My words he hath not performed;' and it is displeasing to Samuel, and he crieth unto Jehovah all the night.
“Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
12 And Samuel riseth early to meet Saul in the morning, and it is declared to Samuel, saying, 'Saul hath come in to Carmel, and lo, he is setting up to himself a monument, and goeth round, and passeth over, and goeth down to Gilgal.'
Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
13 And Samuel cometh in unto Saul, and Saul saith to him, 'Blessed [art] thou of Jehovah; I have performed the word of Jehovah.'
Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
14 And Samuel saith, 'And what [is] the noise of this flock in mine ears — and the noise of the herd which I am hearing?'
Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
15 And Saul saith, 'From Amalek they have brought them, because the people had pity on the best of the flock, and of the herd, in order to sacrifice to Jehovah thy God, and the remnant we have devoted.'
Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
16 And Samuel saith unto Saul, 'Desist, and I declare to thee that which Jehovah hath spoken unto me to-night;' and he saith to him, 'Speak.'
Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
17 And Samuel saith, 'Art not thou, if thou [art] little in thine own eyes, head of the tribes of Israel? and Jehovah doth anoint thee for king over Israel,
Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
18 and Jehovah sendeth thee in the way, and saith, Go, and thou hast devoted the sinners, the Amalekite, and fought against them till they are consumed;
Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
19 and why hast thou not hearkened to the voice of Jehovah — and dost fly unto the spoil, and dost do the evil thing in the eyes of Jehovah?'
Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
20 And Saul saith unto Samuel, 'Because — I have hearkened to the voice of Jehovah, and I go in the way which Jehovah hath sent me, and bring in Agag king of Amalek, and Amalek I have devoted;
Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
21 and the people taketh of the spoil of the flock and herd, the first part of the devoted thing, for sacrifice to Jehovah thy God in Gilgal.'
Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
22 And Samuel saith, 'Hath Jehovah had delight in burnt-offerings and sacrifices as [in] hearkening to the voice of Jehovah? lo, hearkening than sacrifice is better; to give attention than fat of rams;
Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
23 for a sin of divination [is] rebellion, and iniquity and teraphim [is] stubbornness; because thou hast rejected the word of Jehovah, He also doth reject thee from [being] king.'
Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
24 And Saul saith unto Samuel, 'I have sinned, for I passed over the command of Jehovah, and thy words; because I have feared the people, I also hearken to their voice;
Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
25 and now, bear, I pray thee, with my sin, and turn back with me, and I bow myself to Jehovah.'
Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
26 And Samuel saith unto Saul, 'I do not turn back with thee; for thou hast rejected the word of Jehovah, and Jehovah doth reject thee from being king over Israel.'
Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
27 And Samuel turneth round to go, and he layeth hold on the skirt of his upper robe — and it is rent!
Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
28 And Samuel saith unto him, 'Jehovah hath rent the kingdom of Israel from thee to-day, and given it to thy neighbour who is better than thou;
Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
29 and also, the Pre-eminence of Israel doth not lie nor repent, for He [is] not a man to be penitent.'
Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
30 And he saith, 'I have sinned; now, honour me, I pray thee, before the elders of my people, and before Israel, and turn back with me; and I have bowed myself to Jehovah thy God.'
Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
31 And Samuel turneth back after Saul, and Saul boweth himself to Jehovah;
Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
32 and Samuel saith, 'Bring ye nigh unto me Agag king of Amalek,' and Agag cometh unto him daintily, and Agag saith, 'Surely the bitterness of death hath turned aside.'
Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
33 And Samuel saith, 'As thy sword bereaved women — so is thy mother bereaved above women;' and Samuel heweth Agag in pieces before Jehovah in Gilgal.
Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
34 And Samuel goeth to Ramath, and Saul hath gone unto his house — to Gibeah of Saul.
Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
35 And Samuel hath not added to see Saul till the day of his death, for Samuel mourned for Saul, and Jehovah repented that He had caused Saul to reign over Israel.
Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.

< 1 Samuel 15 >