< 2 Chronicles 14 >

1 And Abijah lieth with his fathers, and they bury him in the city of David, and reign doth Asa his son in his stead: in his days was the land quiet ten years.
Abiya kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki, a zamaninsa kuma ƙasar ta zauna lafiya na shekara goma.
2 And Asa doth that which is good, and that which is right, in the eyes of Jehovah his God,
Asa ya yi abin da yake da kyau da kuma daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.
3 and turneth aside the altars of the stranger, and the high places, and breaketh the standing-pillars, and cutteth down the shrines,
Ya kawar da baƙin bagade da masujadai bisa tudu, ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya kuma sassare ginshiƙan Ashera.
4 and saith to Judah to seek Jehovah, God of their fathers, and to do the law and the command;
Ya umarci Yahuda su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kuma yi biyayya da dokoki da kuma umarnansa.
5 and he turneth aside out of all cities of Judah the high places and the images, and the kingdom is quiet before him.
Ya kawar da masujadan kan tudu da bagadan turare a kowane gari a Yahuda, masarautar kuwa ta zauna lafiya a ƙarƙashinsa.
6 And he buildeth cities of bulwarks in Judah, for the land hath quiet, and there is no war with him in these years, because Jehovah hath given rest to him.
Ya gina biranen katanga na Yahuda, da yake ƙasar tana zaman lafiya. Babu wanda yake yaƙi da shi a waɗannan shekaru, gama Ubangiji ya ba shi hutu.
7 And he saith to Judah, 'Let us build these cities, and compass [them] with wall, and towers, two-leaved doors, and bars, while the land [is] before us, because we have sought Jehovah our God, we have sought, and He giveth rest to us round about;' and they build and prosper.
Ya ce wa Yahuda, “Bari mu gina waɗannan garuruwa mu sa katanga kewaye da su, da hasumiyoyi, ƙofofi da ƙyamare. Ƙasar har yanzu tamu ce domin mun nemi Ubangiji Allahnmu, mun neme shi ya kuwa ba mu hutu a kowane gefe.” Saboda haka suka gina suka kuma yi nasara.
8 And there is to Asa a force bearing target and spear, out of Judah three hundred thousand, and out of Benjamin, bearing shield and treading bow, two hundred and eighty thousand: all these [are] mighty of valour.
Asa ya kasance da mayaƙa dubu ɗari uku daga Yahuda, kintsatse da manyan garkuwoyi da māsu, da kuma mayaƙa dubu ɗari biyu da dubu tamanin daga Benyamin, riƙe da ƙananan garkuwoyi da kuma baka. Dukan waɗannan jarumawa ne ƙwarai.
9 And come out unto them doth Zerah the Cushite with a force of a thousand thousand, and chariots three hundred, and he cometh in unto Mareshah,
Zera mutumin Kush ya taka ya fita don yă yaƙe su da babban runduna da kuma kekunan yaƙi ɗari uku, ya kuma zo har Maresha.
10 and Asa goeth out before him, and they set battle in array in the valley of Zephathah at Mareshah.
Asa ya fita don yă ƙara da shi, suka ja dāgā yaƙi a Kwarin Zefata kusa da Maresha.
11 And Asa calleth unto Jehovah his God, and saith, 'Jehovah! it is nothing with Thee to help, between the mighty and those who have no power; help us, O Jehovah, our God, for on Thee we have leant, and in Thy name we have come against this multitude; O Jehovah, our God thou [art]; let him not prevail with Thee — mortal man!
Sai Asa ya kira ga Ubangiji Allahnsa ya ce, “Ubangiji, babu wani kamar ka da zai taimaki marar ƙarfi a kan mai ƙarfi. Ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama mun dogara a gare ka, kuma a cikin sunanka muka fito don mu yaƙi wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum yă yi nasara a kanka.”
12 And Jehovah smiteth the Cushim before Asa, and before Judah, and the Cushim flee,
Ubangiji fa ya bugi mutanen Kush a gaban Asa da Yahuda. Mutanen Kush suka gudu,
13 and Asa and the people who [are] with him pursue them even to Gerar, and there fall of the Cushim, for they have no preserving, because they have been broken before Jehovah, and before His camp; and they bear away very much spoil,
Asa kuwa da mayaƙansa suka bi su har Gerar. Mutanen Kush suka mutu a ranan nan har ba a iya ƙidaya, aka buge su a gaban Ubangiji da rundunansa. Mutanen Yahuda suka kwashi ganima sosai.
14 and smite all the cities round about Gerar, for a fear of Jehovah hath been upon them, and they spoil all the cities, for abundant spoil hath been in them;
Suka hallaka dukan ƙauyukan kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka kwashi ganima na dukan ƙauyukan nan, da yake akwai ganima sosai a can.
15 and also tents of cattle they have smitten, and they capture sheep in abundance, and camels, and turn back to Jerusalem.
Suka kuma yaƙi sansanin makiyaya suka kwashe tumaki da awaki da raƙuma. Suka koma Urushalima.

< 2 Chronicles 14 >