< 1 Chroniques 11 >

1 Tout Israël s’assembla auprès de David à Hébron, en disant: « Voici que nous sommes tes os et ta chair.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 Autrefois déjà, quand Saül était roi, c’était toi qui menais et ramenais Israël. Et Yahweh, ton Dieu, t’a dit: C’est toi qui paîtras mon peuple d’Israël, et c’est toi qui seras chef sur mon peuple d’Israël. »
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 Ainsi tous les anciens d’Israël vinrent auprès du roi à Hébron, et David fit alliance avec eux devant Yahweh, à Hébron; et ils oignirent David pour roi sur Israël, selon la parole de Yahweh prononcée par Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 David marcha avec tout Israël contre Jérusalem, qui est Jébus; là étaient les Jébuséens, habitants du pays.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 Les habitants de Jébus dirent à David: « Tu n’entreras pas ici. » Mais David s’empara de la forteresse de Sion: c’est la cité de David.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 David dit: « Quiconque battra le premier les Jébuséens sera chef et prince. » Joab, fils de Sarvia, monta le premier, et il devint chef.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 David s’établit dans la forteresse; c’est pourquoi on l’appela cité de David.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 Il bâtit la ville tout autour, à partir du Mello et aux environs, et Joab répara le reste de la ville.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David devenait de plus en plus grand, et Yahweh des armées était avec lui.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Voici les chefs des héros qui étaient au service de David, et qui, avec tout Israël, l’aidèrent pendant son règne, après avoir contribué à le faire roi, selon la parole de Yahweh au sujet d’Israël.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 Voici le nombre des héros qui étaient au service de David: Jesbaam, fils de Hachamoni, chef des Trente. Il brandit sa lance sur trois cents hommes, qu’il fit périr en une seule fois.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 Après lui, Eléazar, fils de Dodo, l’Ahohite; il était parmi les trois vaillants.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 Il était avec David à Phes-Domim, et les Philistins s’y étaient rassemblés pour combattre. Il y avait là une pièce de terre pleine d’orge, et le peuple fuyait devant les Philistins.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 Ils se placèrent au milieu du champ, le défendirent et battirent les Philistins; et Yahweh opéra une grande délivrance.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Trois d’entre les trente capitaines descendirent auprès de David sur le rocher, à la caverne d’Odollam, tandis que le camp des Philistins était dressé dans la vallée des Réphaïm.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 David était alors dans la forteresse, et il y avait un poste de Philistins à Bethléem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 David eut un désir, et il dit: « Qui me fera boire de l’eau de la citerne qui est à la porte de Bethléem? »
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Aussitôt les trois hommes, passant au travers du camp des Philistins, puisèrent de l’eau de la citerne qui est à la porte de Bethléem. Ils la prirent et l’apportèrent à David; mais David ne voulut pas la boire, et il en fit une libation à Yahweh,
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 en disant: « Que mon Dieu me garde de faire cela! Boirais-je le sang de ces hommes avec leur vie? Car c’est au péril de leur vie qu’ils l’ont apportée. » Et il ne voulut pas la boire. Voilà ce que firent ces trois braves.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Abisaï, frère de Joab, était chef des Trois; il brandit sa lance contre trois cents hommes et les tua, et il eut du renom parmi les trois.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Il était le plus considéré de la seconde triade, et il fut leur chef; mais il n’égala pas les trois premiers.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Banaïas, fils de Joïada, fils d’un homme vaillant et riche en exploits, de Cabséel. Il frappa les deux ariels de Moab. Il descendit et frappa le lion au milieu de la citerne un jour de neige.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 Il frappa un Egyptien d’une stature de cinq coudées; et dans la main de l’Egyptien, il y avait une lance semblable à une ensouple de tisserand. Il descendit vers lui avec un bâton, et il arracha la lance de la main de l’Egyptien et le frappa de sa propre lance.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Voilà ce que fit Banaïas, fils de Joïada, et il eut du renom parmi les trois vaillants.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Voici qu’il était plus considéré que les trente, mais il n’égala pas les trois. David le fit membre de son conseil secret.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Hommes vaillants de l’armée: Asaël, frère de Joab; Elchanan, fils de Dodo, de Bethléem;
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Sammoth, d’Arori; Hellès, de Phalon;
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Hira, fils d’Accès, de Thécué; Abiéser, d’Anathot;
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sobbochaï, le Husathite; Ilaï, l’Ahohite;
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharaï, de Nétopha; Héled, fils de Baana, de Nétopha;
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ethaï, fils de Ribaï, de Gabaa des fils de Benjamin; Banaïa, de Pharaton;
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Huraï, des vallées de Gaas; Abiel, d’Araba; Azmaveth, de Bauram; Eliaba, de Salabon;
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Bené-Assem, de Gézon; Jonathan, fils de Sagé, d’Arar;
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 Ahiam, fils de Sachar, d’Arar;
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Eliphal, fils d’Ur;
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hépher, de Méchéra; Ahia, de Phélon;
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hesro, de Carmel; Naaraï fils d’Asbaï;
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joël frère de Nathan; Mibahar, fils d’Agaraï;
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Sélec, l’Ammonite; Naharaï, de Béroth, écuyer de Joab, fils de Sarvia;
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira, de Jéther; Gareb, de Jéther;
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Urie, le Hethéen; Zabad, fils d’Oholi;
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina, fils de Siza le Rubénite, chef des Rubénites, et trente avec lui;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan, fils de Maacha; Josaphat, de Mathan;
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Ozia, d’Astaroth; Samma et Jéhiel, fils de Hotham d’Aroër;
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jédihel, fils de Samri; Joha, son frère, le Thosaïte;
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel, de Mahum; Jéribaï et Josaïa, fils d’Elnaëm; Jethma, le Moabite;
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel, Obed et Jasiel, de Masobia.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chroniques 11 >