< Marc 3 >

1 Jésus étant entré une autre fois dans la synagogue, il s'y trouvait un homme qui avait la main desséchée.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 Et on l'observait pour voir s'il le guérirait le jour du sabbat, afin de pouvoir l'accuser.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 Jésus dit à l'homme qui avait la main desséchée: " Tiens-toi là debout au milieu ";
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 puis il leur dit: " Est-il permis le jour du sabbat, de faire du bien ou de faire du mal, de sauver la vie ou de l'ôter? " Et ils se taisaient.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 Alors, les regardant avec indignation, et contristé de l'aveuglement de leur cœur, il dit à cet homme: " Etends ta main. " Il l'étendit, et sa main redevint saine.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 Les Pharisiens, étant sortis, allèrent aussitôt s'entendre contre lui avec les Hérodiens, pour tâcher de le perdre.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Jésus se retira vers la mer avec ses disciples, et une foule nombreuse le suivit de la Galilée, de la Judée,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 de Jérusalem, de l'Idumée et d'au delà du Jourdain. Ceux des environs de Tyr et de Sidon, ayant appris les choses qu'il faisait, vinrent aussi à lui en grande foule.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 Et il dit à ses disciples de tenir toujours une barque à sa disposition, afin qu'il ne fût pas pressé par la foule.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 Car, comme il guérissait beaucoup de gens, tous ceux qui avaient quelque mal se jetaient sur lui pour le toucher.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 Les esprits impurs, en le voyant, se prosternaient devant lui et s'écriaient:
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 " Vous êtes le Fils de Dieu "; mais il leur défendait avec de grandes menaces de faire connaître qui il était.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 Etant monté ensuite sur la montagne, il appela ceux que lui-même voulut; et ils vinrent à lui.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 Il en établit douze pour les avoir avec lui et pour les envoyer prêcher,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 avec le pouvoir de guérir les maladies et de chasser les démons.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 A Simon il donna le surnom de Pierre;
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 puis il choisit Jacques, fils de Zébédée, et Jean, frère de Jacques, auxquels il donna le surnom de Boanergès, c'est-à-dire, fils du tonnerre;
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 André, Philippe, Barthélemy, Matthieu, Thomas, Jacques fils d'Alphée, Thaddée, Simon le Zélé,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 et Judas Iscariote, qui le trahit.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Ils revinrent à la maison, et la foule s'y assembla de nouveau, de sorte qu'ils ne pouvaient pas même prendre leur repas.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 Ce que ses parents ayant appris, ils vinrent pour se saisir de lui, car ils disaient: " Il est hors de sens. "
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 Mais les Scribes, qui étaient venus de Jérusalem, disaient: " Il est possédé de Béelzébub; et c'est par le prince des démons qu'il chasse les démons. "
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 Jésus les appela et leur dit en parabole: " Comment Satan peut-il chasser Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 Si un royaume est divisé contre lui-même, ce royaume ne saurait subsister;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison ne saurait subsister.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 Si donc Satan s'élève contre lui-même, il est divisé, il ne pourra subsister, et sa puissance touche à sa fin.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Nul ne peut entrer dans la maison du fort et enlever ses meubles, si auparavant il ne l'enchaîne; et alors il pillera sa maison.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 En vérité, je vous le dis, tous les péchés seront remis aux enfants des hommes, même les blasphèmes qu'ils auront proférés.
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 Mais celui qui aura blasphémé contre l'Esprit-Saint n'obtiendra jamais de pardon; il est coupable d'un péché éternel. " (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Jésus parla ainsi, parce qu'ils disaient: " Il est possédé d'un esprit impur. "
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 Sa mère et ses frères étant venus, ils se tinrent dehors et l'envoyèrent appeler.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 Or le peuple était assis autour de lui, et on lui dit: " Votre mère et vos frères sont là dehors, qui vous cherchent. "
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 Il répondit: " Qui est ma mère et qui sont mes frères? "
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Puis, promenant ses regards sur ceux qui étaient assis autour de lui: " Voici, dit-il, ma mère et mes frères.
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Car quiconque fait la volonté de Dieu, celui-là est mon frère, et ma sœur et ma mère. "
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Marc 3 >