< 2 Chroniques 23 >

1 Et la septième année, Jehoïada se fortifia, et fit un pacte avec les chefs de centaines, Azaria, fils de Jerokham, et Ismaël, fils de Jokhanan, et Azaria, fils d’Obed, et Maascéïa, fils d’Adaïa, et Élishaphat, fils de Zicri.
A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
2 Et ils firent le tour de Juda, et assemblèrent les lévites de toutes les villes de Juda, et les chefs des pères d’Israël; et ils vinrent à Jérusalem.
Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
3 Et toute la congrégation fit alliance avec le roi dans la maison de Dieu; et [Jehoïada] leur dit: Voici, le fils du roi régnera, selon ce que l’Éternel a dit touchant les fils de David.
dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
4 C’est ici ce que vous ferez: un tiers d’entre vous qui entrez le [jour du] sabbat, sacrificateurs et lévites, sera chargé de la garde des seuils;
Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
5 et un tiers sera dans la maison du roi; et un tiers à la porte de Jesod; et tout le peuple sera dans les parvis de la maison de l’Éternel.
kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
6 Et que personne n’entre dans la maison de l’Éternel, sauf les sacrificateurs et les lévites qui feront le service: eux, ils entreront, car ils sont saints; et tout le peuple fera l’acquit de la charge de l’Éternel.
Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
7 Et les lévites entoureront le roi de tous côtés, chacun ses armes à la main; et celui qui entrera dans la maison sera mis à mort; et soyez avec le roi quand il entrera et quand il sortira.
Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
8 Et les lévites et tout Juda firent selon tout ce que Jehoïada, le sacrificateur, avait commandé; et ils prirent chacun ses hommes, ceux qui entraient le [jour du] sabbat et ceux qui sortaient le [jour du] sabbat; car Jehoïada, le sacrificateur, n’avait pas renvoyé les classes.
Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
9 Et Jehoïada, le sacrificateur, donna aux chefs de centaines les lances, et les écus, et les boucliers, qui avaient appartenu au roi David, et qui étaient dans la maison de Dieu.
Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
10 Et il fit tenir là tout le peuple, chacun sa javeline à la main, depuis le côté droit de la maison jusqu’au côté gauche de la maison, vers l’autel et vers la maison, auprès du roi, tout autour.
Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
11 Et ils firent sortir le fils du roi, et mirent sur lui la couronne et le témoignage; et ils le firent roi; et Jehoïada et ses fils l’oignirent, et dirent: Vive le roi!
Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
12 Et Athalie entendit le cri du peuple qui courait et acclamait le roi, et elle entra vers le peuple dans la maison de l’Éternel.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
13 Et elle regarda, et voici, le roi se tenait sur son estrade, à l’entrée, et les chefs et les trompettes étaient auprès du roi, et tout le peuple du pays se réjouissait et sonnait des trompettes, et les chantres [étaient là] avec des instruments de musique, et ceux qui enseignaient à louer [Dieu]. Et Athalie déchira ses vêtements, et dit: Conspiration! Conspiration!
Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
14 Et Jehoïada, le sacrificateur, fit sortir les chefs de centaines qui étaient préposés sur l’armée, et leur dit: Faites-la sortir en dehors des rangs, et que celui qui la suivra soit mis à mort par l’épée; car le sacrificateur dit: Ne la mettez pas à mort dans la maison de l’Éternel.
Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
15 Et ils lui firent place; et elle alla par l’entrée de la porte des chevaux dans la maison du roi, et là ils la mirent à mort.
Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
16 Et Jehoïada fit une alliance entre lui et tout le peuple et le roi, qu’ils seraient le peuple de l’Éternel.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
17 Et tout le peuple entra dans la maison de Baal, et ils la démolirent; et ils brisèrent ses autels et ses images, et tuèrent devant les autels Matthan, sacrificateur de Baal.
Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
18 Et Jehoïada mit les charges de la maison de l’Éternel entre les mains des sacrificateurs lévites, que David avait établis par classes sur la maison de l’Éternel pour offrir les holocaustes à l’Éternel, comme il est écrit dans la loi de Moïse, avec joie et avec des cantiques, selon les directions de David.
Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
19 Et il plaça les portiers aux portes de la maison de l’Éternel, afin qu’il n’y entre aucune personne impure en quoi que ce soit.
Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
20 Et il prit les chefs de centaines, et les nobles, et ceux qui avaient autorité sur le peuple, et tout le peuple du pays, et il fit descendre le roi de la maison de l’Éternel, et ils entrèrent dans la maison du roi par la porte supérieure; et ils firent asseoir le roi sur le trône du royaume.
Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
21 Et tout le peuple du pays se réjouit, et la ville fut tranquille: et ils avaient mis à mort Athalie par l’épée.
sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.

< 2 Chroniques 23 >