< 1 Samuel 21 >

1 David se rendit à Nomba chez le prêtre Abimélech; Abimélech, étonné de sa venue, lui dit: Pourquoi es-tu seul, et n'y a-t-il personne avec toi?
Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
2 David dit au prêtre: Le roi aujourd'hui m'a donné ce commandement: Que nul ne sache l'affaire pour laquelle je t'envoie, et dont je te charge. J'ai donc convoqué mes serviteurs au lieu dit la Foi de Dieu (Phellani-Maimoni).
Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
3 Maintenant, as-tu sous la main cinq pains? Donne-moi ce que tu pourras trouver.
Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
4 Le prêtre répondit à David, et il lui dit: Je n'ai point sous la main de pains profanes, je n'ai que des pains consacrés; si tes gens se sont au moins abstenus de femmes, ils en peuvent manger.
Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
5 David reprit: Quant aux femmes, depuis trois jours, nous nous en sommes abstenus; lorsque je suis parti, tous mes hommes ont été purifiés; mais la route elle-même les souille; c'est pourquoi nous nous purifions aujourd'hui en lavant nos vêtements.
Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
6 Alors, Abimélech le prêtre lui donna les pains de proposition; car il n'y avait là d'autres pains que ceux qu'on venait d'ôter de devant la face du Seigneur, pour les remplacer par des pains chauds, le jour même où David les prit.
Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
7 Or, il se trouvait là un serviteur de Saül, retenu devant le Seigneur; il se nommait Doeg le Syrien, et il faisait paître les mulets de Saül.
A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
8 Et David dit à Abimélech: Vois si tu as ici sous la main quelque javeline ou quelque épée; car je n'ai pris ni mon glaive ni aucune arme, tant l'affaire du roi exigeait de précipitation.
Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
9 Et le prêtre dit: Voici l'épée de Goliath le Philistin, que tu as vaincu dans le vallon d'Ela; elle est enveloppée dans un manteau; si tu la veux, tu peux l'emporter; hormis cette arme, il n'en est aucune ici. A quoi David répondit: Donne-la-moi; elle n'a pas sa pareille.
Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
10 Le prêtre la lui donna, et David partit. Ce jour-là, il s'enfuit loin de Saül, et il alla chez Achis, roi de Geth.
A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
11 Et les serviteurs d'Achis dirent à leur maître: N'est-ce point là David, le roi de la terre? N'est-ce pas celui dont les danseuses, en chantant, disaient: Saül les a tués par milliers, David les a tués par myriades?
Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
12 Et David pesa ces paroles en son cœur, et il eut grande crainte en présence du roi Achis.
Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
13 Aussitôt, devant lui, il se donna un nouvel aspect, et, ce jour-là, il usa de feinte; il tambourina sur les portes de la ville; il fit de ses mains des gestes insensés; il tomba contre les battants des portes, et l'écume ruisselait sur sa barbe.
Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
14 Et Achis dit à ses serviteurs: Voyez, cet homme est épileptique. Pourquoi me l'avez-vous amené?
Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
15 Ai-je besoin d'épileptiques? A quoi bon l'avoir amené pour qu'il tombe en épilepsie devant moi? Il n'entrera pas dans ma maison.
Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”

< 1 Samuel 21 >