< 2 Rois 22 >

1 Josias avait huit ans quand il monta sur le trône, et il régna trente et un ans à Jérusalem; sa mère se nommait Jedia, fille d'Edia de Basuroth.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 Et il fit ce qui est droit aux yeux du Seigneur; il marcha dans toutes les voies de David, son aïeul; il n'en dévia ni à droite ni à gauche.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 En la troisième année du règne de Josias, le huitième mois, le roi envoya Saphan, fils d'Ezélie, fils de Mésollam, scribe du temple du Seigneur, disant:
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 Monte auprès d'Helcias le grand prêtre; compte l'argent offert par le peuple dans le temple, et recueilli par les gardiens de la porte.
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 Qu'ils remettent cet argent aux ouvriers employés dans le temple. Et l'on donna cet argent aux ouvriers du temple, pour qu'ils y fissent des réparations.
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 On le donna aux charpentiers, aux constructeurs, aux maçons, pour acheter du bois et des pierres de taille, et consolider le temple.
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 Mais on ne leur demanda pas compte de l'argent qui leur fut confié, parce que les travaux furent exécutés de bonne foi.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 Or, le grand prêtre Helcias dit à Saphan le scribe: J'ai trouvé dans le temple le livre de la loi. Et il lui donna le livre; puis, Saphan le lut.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 Ensuite, il entra auprès du roi dans le temple; il lui rapporta ce qui avait été fait, et il dit: Tes serviteurs ont fondu l'argent trouvé dans le temple du Seigneur, et ils l'ont remis aux ouvriers du temple.
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 Et Saphan le scribe ajouta: Le prêtre Helcias m'a donné un livre. Et Saphan le lut devant le roi.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 Quand Josias ouït les paroles du livre de la loi, il déchira ses vêtements,
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 Et il donna ses ordres à Helcias le prêtre, à Achicam, fils de Saphan, à Achobor, fils de Michée, à Saphan le scribe, à Amie, serviteur du roi, et il leur dit:
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 Allez au Seigneur vous enquérir de moi, de tout le peuple, de tout Juda, concernant les paroles de ce livre qu'on a trouvé; car la colère dont le Seigneur s'est enflammé contre nous est grande, parce que nos pères n'ont point écouté les paroles de ce livre pour faire selon ce qui est écrit à notre sujet.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 Et le prêtre Helcias, Achicam, Achobor, Saphan et Asaïe, allèrent chez la prophétesse Olda, mère de Sellem, fils de Thécuan, fils d'Aras, gardien des vêtements. Elle demeurait à Jérusalem dans le quartier de Masena, et ils lui parlèrent.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 Et elle leur répondit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël: Dites à l'homme qui vous a envoyés près de moi:
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 Voici ce que dit le Seigneur: Voilà que j'apporte des maux à ce lieu et à ceux qui l'habitent, selon les paroles du livre qu'a lu le roi de Juda;
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 En punition de ce qu'ils m'ont abandonné, et de ce qu'ils ont encensé d'autres dieux, de sorte qu'ils m'ont irrité par toutes les œuvres de leurs mains; car ma colère est enflammée contre ce lieu, et elle ne s'éteindra pas.
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 Quant au roi de Juda, qui vous a envoyés vous enquérir au Seigneur, dites-lui: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël au sujet des paroles que tu as entendues:
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 En récompense de ce que ton cœur ne s'est point endurci, de ce que devant moi tu es rentré en toi-même quand tu as ouï ce que j'ai dit contre ce lieu et contre ceux qui l'habitent, pour qu'ils soient effacés et maudits; de ce que tu as déchiré tes vêtements et pleuré en ma présence: eh bien! moi aussi j'ai entendu, dit le Seigneur.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Il n'en sera pas ainsi: voilà que je te réunis à tes pères; tu descendras en paix dans ton sépulcre, et tes yeux ne verront aucun des maux que j'apporte en ce lieu.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Rois 22 >