< Deutéronome 31 >

1 Et Moïse acheva de dire toutes ces paroles à tous les fils d'Israël.
Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
2 Et il leur dit: J'ai cent vingt ans, je ne pourrai plus bientôt entrer ni sortir; et le Seigneur m'a dit: Tu ne passeras pas le Jourdain.
“Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
3 Le Seigneur ton Dieu qui marche à ta tête, exterminera lui-même ces nations à ton aspect, et tu prendras possession de leur héritage par les soins de Josué, qui va marcher à ta tête, comme l'a prescrit le Seigneur.
Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
4 Et le Seigneur ton Dieu les traitera, elles et leur terre, comme il a traité Séhon et Og, les deux rois des Amorrhéens, en deçà du fleuve; il les exterminera comme il les a exterminés.
Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
5 Le Seigneur vous les a livrées, et vous leur ferez ce que j'ai prescrit.
Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
6 Sois fort et agis en homme, n'aie ni crainte ni faiblesse; ne te laisse pas frapper de stupeur devant elles, car le Seigneur ton Dieu, qui marche parmi nous, ne t'a point abandonné ni délaissé.
Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, ba zai taɓa barinku ko yă yashe ku ba.”
7 Et Moïse appela Josué, et il lui dit devant tout Israël: Sois fort, agis en homme; car tu entreras, à la tête de ce peuple, en la terre que le Seigneur a promis à vos pères de leur donner, et tu la partageras entre les tribus.
Sai Musa ya kira Yoshuwa, ya ce masa a gaban dukan Isra’ila, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama dole ka tafi tare da mutanen nan zuwa cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse cewa za ba wa kakanninku, dole kuma ka raba ta gare su ta zama gādonsu.
8 Le Seigneur, qui marche parmi nous, ne t'abandonnera pas, et il ne t'a pas délaissé; n'aie ni crainte, ni faiblesse.
Ubangiji kansa yana tafe a gabanka, zai kuma kasance tare da kai, ba zai taɓa barinka ko yă yashe ka ba. Kada ka ji tsoro; kada kuma ka karai.”
9 Moïse écrivit les paroles de cette loi en un livre, et il le donna aux prêtres fils de Lévi, qui transportent l'arche de l'alliance du Seigneur, ainsi qu'aux plus anciens des fils d'Israël.
Sai Musa ya rubuta wannan doka ya kuma ba da ita ga firistoci,’ya’yan Lawi maza, waɗanda sukan ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji, da kuma dukan dattawan Isra’ila.
10 Et Moïse, en ce jour-là, leur donna des ordres, et il dit: Après sept ans, l'année de la rémission, pendant la fête des tabernacles,
Sa’an nan Musa ya umarce su ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a shekara ta yafe basusuwa, a lokacin Bikin Tabanakul,
11 Lorsque tout Israël se sera rassemblé pour comparaître devant le Seigneur notre Dieu, au lieu qu'aura choisi le Seigneur, vous lirez cette loi devant tout Israël, qui se tiendra attentif,
sa’ad da dukan Isra’ila suka zo, don su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa, za ku karanta wannan doka a gabansu, a kunnuwansu.
12 Lorsque tout le peuple: hommes, femmes, enfants, étranger établi en vos villes, sera réuni; afin qu'il l'entende et qu'il apprenne à craindre le Seigneur; et ils seront instruits à obéir à toutes les paroles de cette loi.
Ku tattara mutane, maza, mata da kuma yara, da baƙin da suke zama a cikin garuruwanku, saboda su saurara, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su lura, su bi dukan kalmomin wannan doka.
13 Et leurs fils qui l'ignoreront encore écouteront et apprendront à craindre le Seigneur votre Dieu, tous les jours qu'ils vivront sur la terre au delà du Jourdain, en laquelle vous allez entrer pour qu'elle soit votre héritage.
’Ya’yansu, waɗanda ba su san wannan doka ba, dole su ji ta, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku muddin ranku a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
14 Et le Seigneur dit à Moïse: Voilà que le jour de ta mort est venu, appelle Josué; tenez-vous devant la porte du tabernacle du témoignage, pour que je lui donne mes ordres. Et ils se tinrent devant la porte du tabernacle du témoignage.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu ranar mutuwarka ta yi kusa. Ka kira Yoshuwa, ku shigo Tentin Sujada, inda zan ba shi ragamar aiki.” Saboda haka Musa da Yoshuwa suka zo, suka kuma shiga Tentin Sujada.
15 Alors, le Seigneur descendit en une nuée, et il s'arrêta devant la porte du tabernacle du témoignage, et la colonne de nuée demeura devant la porte du tabernacle du témoignage.
Ubangiji kuwa ya bayyana a Tentin Sujada a cikin ginshiƙin girgije, sai girgijen ya tsaya a ƙofar Tentin Sujada.
16 Puis, le Seigneur dit à Moïse: Voilà que tu vas dormir avec tes pères, et ce peuple se lèvera, et il se prostituera à la suite des dieux étrangers de la terre où il entre; ils me délaisseront, et ils déchireront l'alliance que j'ai faite avec eux.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Za ka huta tare da kakanninka, waɗannan mutane kuwa ba da daɗewa ba za su yi karuwanci ga baƙin alloli na ƙasar da za su shiga. Za su yashe ni su kuma karya alkawarin da na yi da su.
17 En ce jour-là, je serai enflammé de colère et je les abandonnerai, et je détournerai d'eux mon visage; et ce peuple sera dévoré; en ce jour-là, des maux sans nombre, des afflictions s'empareront de lui; et il dira: Ces maux me sont venus parce que le Seigneur n'est pas avec moi.
A wannan rana zan yi fushi da su, in kuma yashe su; zan ɓoye fuskata daga gare su, za a kuwa hallaka su. Masifu masu yawa da wahaloli masu yawa za su auka musu, a wannan rana kuwa za su ce, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu’
18 Pour moi, en ce jour-là, je détournerai d'eux mon visage à cause de tous les vices auxquels ils se seront adonnés, car ils se seront pervertis avec des dieux étrangers.
Tabbatacce kuwa, zan ɓoye musu fuskata saboda muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.
19 Ecrivez donc les paroles de ce cantique, et enseignez-le aux fils d'Israël, et faites-le passer par leur bouche, afin que, devant moi, ce cantique porte témoignage pour les fils d'Israël.
“To, sai ka rubuta wannan waƙa domin kanka, ka koya wa Isra’ilawa, ka kuma sa su rera ta, don tă zama shaida a kansu.
20 Je les introduirai dans cette terre fortunée que j'ai promis à leurs pères de leur donner, terre où coulent le lait et le miel; et ils mangeront, et, s'étant repus, ils sentiront la satiété, et ils s'égareront avec les dieux étrangers; ils les serviront, ils m'irriteront et déchireront mon alliance.
Sa’ad da na kawo su cikin ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa ga kakanninsu, sa’ad da kuma suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba, za su juya ga waɗansu alloli su bauta musu, su ƙi ni, su kuma karya alkawarina.
21 Mais ce cantique portera témoignage devant moi; en effet, ni leur bouche, ni la bouche de leur race ne l'oublieront tout à fait; et moi, je sais leur malice et ce qu'ils feront aujourd'hui même, avant que je les aie introduits en cette terre fortunée que j'ai promise à leurs pères.
Sa’ad da kuma masifu masu yawa da wahaloli masu yawa suka auko musu, wannan waƙa za tă zama shaida a kansu, domin zuriyarsu ba za tă manta da ita ba. Na san abin da za su iya yi, kafin ma in kawo su cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa.”
22 En ce jour-là donc, Moïse écrivit ce cantique, et il l'apprit aux fils d'Israël.
Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a wannan rana, ya kuma koya wa Isra’ilawa.
23 Et il donna des ordres à Josué, et il lui dit: Sois fort et agis en homme, car tu vas conduire les fils d'Israël en la terre que le Seigneur leur a promise, et le Seigneur sera avec toi.
Ubangiji ya ba wa Yoshuwa ɗan Nun wannan umarni, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama za ka kawo Isra’ilawa cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa, ni kaina kuwa zan kasance tare da kai.”
24 Or, quand Moïse eut achevé d'écrire, jusqu'au dernier mot, toutes les paroles de cette loi, en un livre,
Bayan Musa ya gama rubuta kalmomin dokan nan a littafi daga farko zuwa ƙarshe,
25 Il donna ces ordres aux lévites qui transportent l'arche de l'alliance du Seigneur, et il leur dit:
sai ya ba wa Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji wannan umarni,
26 Prenez le livre de cette loi, déposez-le sur les côtés de l'arche de l'alliance du Seigneur votre Dieu, et là, il sera pour vous un témoignage.
“Ku ɗauki wannan Littafin Doka ku sa shi kusa da akwatin alkawarin Ubangiji Allahnku. A can zai kasance a matsayin shaida a kanku.
27 Je connais, ô Israël, votre humeur provoquante, votre entêtement; je sais qu'aujourd'hui même, tandis que je vis encore parmi vous, vous êtes aigris contre les choses du Seigneur; comment donc ne le seriez-vous pas après ma mort?
Gama na sani yadda kuke’yan tawaye da masu taurinkai. In kuna yin tawaye ga Ubangiji tun ina da rai tare da ku, yaya tawayen da za ku yi masa bayan na rasu!
28 Amenez-moi vos chefs de tribus, vos anciens, vos juges, vos scribes, afin qu'à leurs oreilles je dise toutes ces paroles, et je prendrai à témoin le ciel et la terre.
Ku tattara dukan dattawan kabilanku, da kuma dukan hafsoshinku a gabana, saboda in faɗa waɗannan kalmomi a kunnuwansu, in kuma kira ga sama da ƙasa su zama shaida a kansu.
29 Car, je sais qu'aussitôt après ma mort, vous vous abandonnerez à l'iniquité et vous vous écarterez de la voie que je vous ai tracée; et peu de jours après, les maux fondront sur vous, parce que vous aurez fait le mal devant le Seigneur, jusqu'à l'irriter contre vos mauvaises œuvres.
Gama na san cewa bayan rasuwata, tabbatacce za ku lalace gaba ɗaya, ku juye daga hanyar da na umarce ku. A kwanaki masu zuwa, masifa za tă auka muku saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, ku tsokane shi har yă yi fushi ta wurin abin da hannuwanku suka yi.”
30 Et, aux oreilles de l'Eglise, Moïse prononça les paroles de ce cantique jusqu'à la fin.
Sai Musa ya karanta kalmomin waƙar daga farko zuwa ƙarshe a kunnuwan dukan taron jama’ar Isra’ila.

< Deutéronome 31 >