< Isaïe 30 >

1 Malheur à vous, enfants rebelles! dit le Seigneur; vous avez tenu conseil, et ce n'est pas avec moi; vous avez pris des résolutions, et ce n'est pas avec mon Esprit; vous entassez péchés sur péchés,
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 O vous qui êtes partis pour descendre en Égypte, sans me consulter, pour demander du secours au Pharaon, et trouver un abri chez les Égyptiens.
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 Car l'appui du Pharaon sera pour vous une honte; et l'opprobre attend ceux qui se reposent sur l'Égypte.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Car vos princes sont allés à Tanis, messagers de malheur.
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 Ils ont pris une peine inutile auprès d'un peuple qui ne les aidera point pour le secours, mais pour la confusion et l'opprobre.
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Ils vont dans l'affliction et la détresse, là où il y a un lion et un lionceau, et d'où viennent aussi des aspics et des petits d'aspics volants; ils ont transporté sur des ânes et des chamelles leurs richesses près d'une nation qui ne les aidera point.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Les Égyptiens vous donneront un secours vain et inutile; dis-leur: Cette consolation pour vous est vaine.
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Maintenant donc, assieds-toi; écris ces choses sur le buis et dans un livre; car ce sera pour les jours de l'avenir et même pour tous les siècles.
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 Parce que ce peuple est indocile; fils menteurs, qui ne veulent point écouter la loi de Dieu,
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 Ils disent aux prophètes: Ne nous annoncez rien; ils disent à ceux qui ont des visions: Ne nous parlez pas; mais annoncez-nous quelque autre erreur.
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 Détournez-nous de cette voie; ôtez-nous le sentier, ôtez-nous l'oracle d'Israël.
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 A cause de cela, voici ce que dit le Saint d'Israël: Parce que vous n'avez point obéi à ces paroles, parce que vous avez espéré dans le mensonge, parce que vous avez murmuré et que vous avez mis votre confiance en vos murmures;
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 A cause de cela, ce péché sera pour vous comme un mur qui s'écroule soudain, lorsque est prise une ville dont la chute est inopinée.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 Et sa chute sera comme quand on brise un vase de poterie; les fragments en sont tels qu'on n'y peut trouver un tesson à transporter du feu, ou à puiser un peu d'eau.
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Voici ce que dit le Seigneur, le Seigneur saint d'Israël: Lorsque après t'être perverti tu te lamenteras, tu seras sauvé, et tu sauras où tu étais; car tu croyais en des vanités, des vanités étaient ta force, et tu n'as pas voulu m'entendre.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 Mais vous avez dit: nous fuirons à cheval; à cause de cela, vous fuirez. Vous avez dit: Nous serons sur des chevaux agiles; à cause de cela, ils seront agiles aussi les chevaux qui vous poursuivront.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Mille des vôtres fuiront à la voix d'un seul ennemi; une multitude fuira à la voix de cinq hommes, jusqu'à ce que vous restiez comme un mât sur une montagne, ou comme la hampe qui porte un étendard sur une colline.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 Et Dieu vous attendra encore pour vous prendre en compassion; et en cela il signalera sa gloire en vous faisant miséricorde; car le Seigneur votre Dieu est le juge. Heureux ceux qui l'attendent!
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Car le peuple saint demeurera en Sion, et Jérusalem pleurera à chaudes larmes, disant: Ayez pitié de moi! Et le Seigneur aura pitié de toi, quand il t'aura vue crier et qu'il t'aura entendue.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Et le Seigneur vous donnera le pain de l'affliction et l'eau de la détresse; et ceux qui t'égarent n'approcheront plus de toi; car tes yeux verront ceux qui t'égarent.
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 Et tes oreilles entendront les discours de ceux qui, derrière toi, t'auront égarée, disant: Voici la voie, suivons-la, soit à droite, soit à gauche.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Alors tu souilleras les idoles argentées, et tu réduiras en poudre les idoles d'or, et tu les jetteras au loin comme l'eau des menstrues, et tu les repousseras comme la fange.
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Alors il tombera de la pluie sur les grains que tu auras semés; alors le pain des fruits de la terre sera plantureux et succulent. Et en ce jour tout bétail broutera dans des pâturages spacieux et fertiles.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Et vos taureaux et vos bœufs de labour mangeront de la paille assaisonnée d'orge vannée.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 Et en ce jour l'eau coulera sur toute haute montagne, sur toute colline élevée, longue beaucoup d'hommes auront péri et que leurs tours seront tombées.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Et la lumière de la lune sera comme la lumière du soleil; et la lumière du soleil sera septuple durant le jour, lorsque le Seigneur aura pansé les meurtrissures de son peuple, et guéri les douleurs de ses plaies.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Voici que le nom du Seigneur arrive après un long temps; sa fureur est ardente; la parole de ses lèvres est pleine de gloire; sa parole est pleine de colère, et les transports de sa fureur dévorent comme le feu.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 Et son souffle, comme l'eau qui se précipite dans un vallon, montera jusqu'au cou; et il se divisera pour troubler les nations au sujet de leurs vaines erreurs; et l'erreur aussi les poursuivra, et les prendra en face.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Ne devrez-vous pas alors être toujours en joie, et toujours entrer dans mes lieux saints, comme aux jours de fête? Ne devrez-vous pas, comme ceux qui se réjouissent, venir au son des flûtes sur la montagne du Seigneur, devant le Dieu d'Israël?
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 Et le Seigneur fera entendre sa voix glorieuse, et la fureur de son bras, qui se manifestera par des transports de colère et une flamme dévorante; sa foudre éditera violemment comme de l'eau et de la grêle qui tombe avec impétuosité.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 Car les Assyriens seront vaincus à la voix du Seigneur, par la plaie dont il les frappera.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 Et c'est là ce qui lui arrivera de tous les alentours, de toute contrée d'où il espérait du secours, et en qui il se confiait; les peuples, au contraire, viendront le combattre au son des tambours et des cithares.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Car vous serez requis avant le temps, Seigneur; tout n'est-il pas préparé pour votre règne, un ravin profond, des arbres abattus, le feu et un vaste bûcher? La colère du Seigneur est comme une vallée embrasée par le soufre.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Isaïe 30 >