< Isaïe 1 >

1 Vision d'Isaïe, fils d'Amos, qu'il eut sur la Judée et Jérusalem, sous le règne d'Ozias et de Joatham, d'Achaz et d'Ézéchias, qui furent rois de la Judée.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Écoute, ciel; prête l'oreille, terre, parce que le Seigneur a parlé, disant: J'ai engendré des fils, et je les ai élevés en gloire; mais eux, ils m'ont méprisé.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 Le bœuf connaît son possesseur, et l'âne, la crèche de son maître; pour Israël, il m'a méconnu, et son peuple ne m'a pas compris.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Malheur à toi, peuple pécheur, nation pleine de péchés, race de méchants, fils pervertis! vous avez abandonné le Seigneur, et irrité le Saint d'Israël.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 A quoi bon vous frapper encore, en ajoutant à votre iniquité? Toute tête est en souffrance, et tout cœur en tristesse.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 Des pieds à la tête, rien n'est sain en lui, rien qui ne soit contusion, meurtrissure, plaie enflammée; point d'émollients à y appliquer, point d'huile, point de ligature.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Votre terre est déserte, vos villes consumées par le feu; votre contrée, des étrangers la dévorent sous vos yeux; elle est désolée et bouleversée par des nations étrangères.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 La fille de Sion sera délaissée comme une tente dans une vigne, comme la cabane d'un garde dans un champ de concombres, comme une ville prise d'assaut.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 Et si le Seigneur des armées ne nous eût laissé une semence, nous serions comme Sodome, nous ressemblerions à Gomorrhe.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Ecoutez la parole du Seigneur, princes de Sodome; soyez attentifs à la loi de Dieu, peuple de Gomorrhe.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 Qu'ai-je besoin de la multitude de vos victimes? Je suis rassasié des holocaustes de béliers; la graisse des agneaux, le sang des taureaux et des boucs, je n'en veux plus.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 Ne venez plus vous montrer à moi; car qui vous a demandé ces offrandes de vos mains? Ne continuez plus de fouler mon parvis.
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Quand vous m'apportez de la fleur de farine, ou un encens inutile, c'est pour moi une abomination. Vos nouvelles lunes, vos sabbats, votre grand jour, je ne puis les souffrir; votre jeûne, votre repos,
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 Vos nouvelles lunes, vos fêtes, mon âme les déteste. Je vous ai en dégoût, je ne vous remettrai plus vos péchés.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 Si vous étendez la main, je détournerai de vous mes yeux; et si vous multipliez vos prières, je ne vous écouterai pas; car vos mains sont pleines de sang.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Lavez-vous, soyez purs; ôtez de devant mes yeux la malice de vos âmes; mettez fin à vos méfaits.
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 Apprenez à faire le bien, cherchez la justice, protègez l'opprimé; jugez équitablement l'orphelin, rendez justice à la veuve.
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 Et puis venez m'accuser, dit le Seigneur. Et quand même vos péchés seraient comme la pourpre, je les rendrai blancs comme la neige; et quand ils seraient comme de l'écarlate, je les rendrai blancs comme une toison.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 Et si vous êtes de bonne volonté, si vous m'écoutez, vous mangerez les biens de la terre.
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 Mais si vous n'êtes point de bonne volonté, si vous ne m'écoutez point, le glaive vous dévorera; car voici ce qu'a dit la bouche du Seigneur:
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 Comment est devenue prostituée Sion, la cité fidèle, jadis pleine de justice? L'équité reposait en elle, et maintenant ce sont des meurtriers.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Votre argent n'est pas de bon aloi; vos cabaretiers mêlent de l'eau à leur vin.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Vos princes sont incrédules, associés aux voleurs, amis des présents, gagnés par les salaires, sans justice pour les orphelins, sans égard pour la cause des veuves.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 C'est pourquoi voici ce que dit le Seigneur, maître des armées: Malheur aux puissants d'Israël! car ma fureur contre mes adversaires ne s'apaisera point, et je tirerai vengeance de mes ennemis.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 Et je ferai tomber ma main sur toi, et je te purifierai par le feu; et j'exterminerai les incrédules, et j'enlèverai tous les prévaricateurs loin de toi.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 Et je rétablirai tes juges comme autrefois, et tes conseillers comme dès le commencement. Et après cela tu seras appelée Ville de justice, métropole fidèle, Sion.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Car ses captifs seront délivrés par le jugement et par la miséricorde.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 Et les méchants seront écrasés, et avec eux les pécheurs; et ceux qui auront abandonné le Seigneur périront avec eux.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 C'est pourquoi ils seront confondus par les idoles mêmes qu'ils avaient voulues, et ils rougiront des jardins qu'ils avaient convoités.
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 Car ils seront comme un térébinthe dépouillé de ses feuilles, et comme un jardin sans eau.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 Et leur force sera comme le chaume du concombre, et leurs œuvres comme des étincelles, et les méchants seront consumés, et avec eux le pécheur; et nul ne sera là pour éteindre la flamme.
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Isaïe 1 >