< Joël 1 >

1 Parole du Seigneur qui vint à Joël, fils de Bathuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Écoutez ce que je vais dire, vieillards; prêtez l'oreille, vous tous qui habitez la terre: Est-il rien arrivé de pareil, soit de nos jours, soit du temps de nos pères?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Plus que vos pères, vous aurez à raconter à vos enfants, et plus encore vos enfants à leurs enfants, et ceux-ci plus encore à la génération suivante.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 La sauterelle a dévoré ce qu'avait laissé la chenille; la grosse sauterelle a dévoré ce qu'avait laissé la sauterelle; la nielle a dévoré ce qu'avait laissé la grosse sauterelle.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Réveillez-vous, ô vous qui vous enivrez de votre vin, et pleurez. Lamentez- vous, ô vous qui buvez du vin jusqu'à l'ivresse; car la gaieté et la joie sont ôtées de vos lèvres.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Une nation puissante et innombrable est montée sur ma terre; ses dents sont des dents de lion, et ses mâchoires des mâchoires de lionceaux.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 Elle a rasé ma vigne, elle a brisé mon figuier, elle a cherché ma vigne et l'a tout arrachée; elle a pelé les rameaux de mon figuier.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Pleurez avec moi, plus que la jeune femme ceinte d'un cilice ne pleure l'époux de sa virginité.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 La victime et les libations ont été enlevées du temple du Seigneur; pleurez, prêtres, qui serviez l'autel du Seigneur;
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 car les champs sont désolés. Que la terre soit en deuil, car le blé manque, les sources du vin sont desséchées, l'olivier est stérile,
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 les laboureurs sont épuisés. Pleurez vos richesses, votre froment, votre orge; car dans les champs la récolte a péri.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 La vigne a été desséchée, les figuiers ont perdu leur fertilité; le grenadier, le palmier, le pommier, tous les arbres fruitiers de la campagne sont morts, parce que les fils des hommes sont confondus dans leur joie.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Prêtres, ceignez-vous, frappez-vous la poitrine; pleurez, vous qui servez à l'autel. Entrez et dormez avec vos cilices, ministres de Dieu, parce que les victimes et les libations sont ravies au temple de Dieu.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Sanctifiez le jeûne, proclamez le service du Seigneur; rassemblez dans le temple de notre Dieu les anciens de tout le peuple de la terre, et criez sans relâche au Seigneur
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Malheur, malheur, malheur en ce jour! Car le jour du Seigneur approche, et il viendra comme une calamité naissant d'une calamité.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Sous vos yeux, votre subsistance a été détruite; et les réjouissances et la joie ont disparu du temple de votre Dieu.
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Les génisses ont bondi devant leurs crèches vides; les trésors de vos granges sont dissipés; les pressoirs sont détruits; les froments desséchés.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Que mettrons-nous en réserve pour nous? Les bœufs du troupeau ont mugi, parce qu'ils n'avaient plus de pâturage, et les petits des agneaux ont entièrement péri.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Je crierai vers Toi, Seigneur; car le feu a consumé les beautés du désert, et la flamme tous les arbres des champs.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Et les bêtes de la plaine ont tourné les yeux vers Toi, parce que les cours d'eau étaient à sec, et que le feu a dévoré les beautés du désert.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joël 1 >