< Juges 1 >

1 Il advint, après la mort de Josué, que les fils d'Israël consultèrent le Seigneur, disant: Quel chef nous conduira contre les Chananéens pour les combattre?
Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
2 Et le Seigneur dit: Juda marchera; voilà que j'ai mis en sa main la terre promise.
Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
3 Et Juda dit à Siméon, son frère: Viens avec moi sur mes terres, et nous livrerons bataille aux Chananéens, ensuite j'irai avec toi sur ton territoire. Et Siméon marcha avec lui.
Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
4 Juda partit donc, et le Seigneur livra à ses mains le Chananéen et le Phérézéen; il les tailla en pièces à Bézec au nombre de dix mille.
Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
5 Après avoir surpris à Bézec Adonibézec, ils lui livrèrent bataille, et taillèrent en pièces le Chananéen et le Phérézéen.
A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
6 Adonibézec prit la fuite, ils coururent après lui, l'atteignirent et lui coupèrent les extrémités des pieds et des mains.
Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
7 Alors, Adonibézec dit: Soixante-dix rois à qui j'avais fait couper les extrémités des pieds et des mains, ont ramassé ce qui tombait sous ma table. Dieu m'a donc traité comme j'ai traité autrui. Et ils le conduisirent à Jérusalem, où il mourut.
Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
8 Et, les fils de Juda assiégèrent Jérusalem; ils la prirent, ils passèrent les habitants au fil de l'épée, et ils incendièrent la ville.
Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
9 Après cela, les fils de Juda descendirent pour combattre le Chananéen qui habitait les montagnes du midi et la plaine.
Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
10 Et Juda marcha contre le Chananéen qui habitait Hébron, et tout Hébron sortit à sa rencontre; le nom d'Hébron était autrefois Cariath-Arboc-Sépher; Juda vainquit Sessi, Achiraan et Tholmi, de la race d'Enac.
Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
11 De là, il monta pour attaquer Dabir; or, le nom de Dabir était autrefois Cariath-Sépher, ou Ville des Lettres.
Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
12 Et Caleb dit: Celui qui montera à l'assaut de la Ville des Lettres et la prendra, je lui donnerai pour femme ma fille Ascha.
Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
13 Et Gothoniel, fils de Cénez, frère puîné de Caleb, prit la ville; et Caleb lui donna pour femme sa fille Ascha.
Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
14 Tandis qu'elle s'en allait, Gothoniel lui persuada de demander à son père un champ, et, montée sur son âne, elle murmura et cria: Tu m'as établie en une terre du midi. Et Caleb lui dit: Qu'as-tu?
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
15 Et Ascha lui dit: Accorde-moi un bienfait; tu m'as établie en une terre du midi; tu me donneras une terre arrosée d'eau - Et Caleb lui donna, selon son cœur, une terre arrosée en haut et en bas.
Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
16 En ce temps-là, les fils de Jéthro le Cinéen, beau-père de Moïse, montèrent de la Ville des Palmiers, pour se réunir aux fils de Juda, dans le désert, au midi de Juda, vers la descente d'Arad, et ils demeurèrent parmi le peuple.
Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
17 Ensuite, Juda marcha avec son frère Siméon; ils vainquirent le Chananéen qui habitait en Sépheth, ils l'exterminèrent, et ils donnèrent à cette ville le nom d'Anathème.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
18 Mais Juda ne prit possession ni de Gaza, ni de son territoire; ni d'Ascalon, ni de son territoire; ni d'Accaron, ni de son territoire; ni d'Asor, ni de son territoire.
Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
19 Toutefois, le Seigneur était avec Juda; il eut dans son héritage la contrée montagneuse, mais il ne put exterminer les habitants de la côte, parce que Rhéchab s'y opposait.
Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
20 Quant à Caleb, on lui avait donné, selon l'ordre de Moïse, le territoire d'Hébron, où il eut dans son héritage les trois villes des fils d'Enac.
Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
21 Les fils de Benjamin ne purent s'emparer du territoire des Jébuséens qui habitaient Jérusalem; les Jebuséens, jusqu'à ce jour, ont donc habité Jérusalem avec les fils de Benjamin.
Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
22 De leur côté, les fils de Joseph montèrent à Béthel, et le Seigneur était avec eux,
To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
23 Et, après avoir établi leur camp, ils reconnurent Béthel, dont le nom était autrefois Luza.
Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
24 Or, les gardes virent un homme qui sortait de la ville; ils le prirent, et ils lui dirent: Montre-nous par où l'on peut entrer dans la ville, et nous serons miséricordieux envers toi.
’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
25 Et il leur montra l'entrée de la ville, et ils passèrent la ville au fil de l'épée, et ils laissèrent aller l'homme avec toute sa famille.
Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
26 L'homme s'en alla dans la terre d'Heltim; il y bâtit une ville, et il lui donna le nom de Luza, qu'elle porte encore de nos jours.
Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
27 Manassé ne détruisit ni Bethsan, qui est une ville des Scythes; ni ses filles, ni ses alentours; ni Thanac, ni ses dépendances; ni les habitants de Dor, ni leurs dépendances; ni l'habitant de Balac, ni ses filles, ni ses dépendances; ni Magedo, ni ses filles, ni ses alentours; ni Jéblaam, ni ses filles, ni ses alentours. Les Chananéens commencèrent à habiter cette terre avec eux.
Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
28 Mais, lorsque Israël eut pris des forces, il assujettit le Chananéen au tribut, quoiqu'il ne le détruisit pas.
Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
29 Ephraïm ne détruisit pas le Chananéen qui habitait Gazer; le Chananéen continua de demeurer à Gazer avec lui, et lui paya un tribut.
Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
30 Zabulon ne détruisit pas les habitants de Cédron, ni ceux de Domana. Le Chananéen continua de demeurer avec lui, et devint son tributaire.
Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
31 Aser ne détruisit pas les habitants d'Accho; ils devinrent ses tributaires; il ne détruisit pas les habitants de Dor, ni ceux de Sidon, de Dalaph, d'Aschazi, de Chebda, de Naï et d'Eréo.
Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
32 Aser demeura au milieu des Chananéens qui habitaient cette terre, parce qu'il ne put les détruire.
kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
33 Nephthali ne détruisit pas les habitants de Bethsamys, ni ceux de Béthanath; Nephthali demeura au milieu du Chananéen qui habitait la contrée. Ceux de Bethsamys et de Béthanath devinrent ses tributaires.
Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
34 L'Amorrhéen resserra Dan sur les montagnes; il ne lui permit pas de descendre dans les vallées.
Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
35 Les Amorrhéens commencèrent même à habiter la montagne de l'Argile, où il y a des ours et des renards; ils eurent Myrsinon et Thalabin; mais la main de la maison de Joseph s'appesantit sur l'Amorrhéen, et celui-ci devint son tributaire.
Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
36 Les limites de l'Amorrhéen furent la montée d'Acrabin, les rochers et les hauteurs qui les dominent.
Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.

< Juges 1 >