< Juges 20 >

1 Tous les fils d'Israël sortirent, depuis Dan jusqu'à Bersabée, y compris la terre de Galaad; la synagogue se réunit comme un seul homme devant le Seigneur à Massépha.
Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
2 Toutes les tribus d'Israël se formèrent devant le Seigneur, en assemblée du peuple de Dieu, au nombre de quatre cent mille hommes à pied, en état de porter les armes.
Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
3 Or, les fils de Benjamin apprirent que les fils d'Israël étaient allés en Massépha; ils y vinrent, et les fils d'Israël leur dirent: Expliquez-vous: où ce crime a-t-il été commis?
(Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
4 Le lévite, le mari de la femme tuée répondit et il dit: J'étais entré avec ma femme à Gabaa en Benjamin, pour y passer la nuit.
Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
5 Quand les hommes de Gabaa se levèrent contre moi; ils m'entourèrent dans la maison ou j'étais logé, voulant me mettre à mort, et ils ont outragé ma femme, et elle en est morte.
Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
6 Je l'ai saisie, je l'ai couple en morceaux, et je l'ai envoyée sur toute l'étendue de l'héritage des fils d'Israël, parce qu'une souillure et une abomination ont été commises en Israël.
Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
7 Voyez donc, ô vous tous fils d'Israël, tenez ici conseil, et parlez.
To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
8 Et tout le peuple se leva comme un seul homme, disant: Nul de nous ne retournera en sa ville, nul de nous ne rentrera dans sa maison.
Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
9 Dès maintenant, voilà ce qu'il faut faire contre Gabaa. Ceux que le sort va désigner marcheront sur cette ville.
Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
10 Nous prendrons dix hommes sur cent de toutes les tribus d'Israël, cent sur mille, mille sur dix mille; nous les approvisionnerons de vivres, et nous les ferons partir pour Gabaa en Benjamin, afin qu'ils la traitent comme le mérite l'abomination qu'elle a commise en Israël.
Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
11 Et tout Israël s'était assemblé contre la ville comme un seul homme,
Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
12 Et les tribus d'Israël envoyèrent, dans toute la tribu de Benjamin, des hommes qui dirent: Quel est le forfait qui a été commis parmi vous?
Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
13 Maintenant, livrez-nous ces hommes, fils de pervers, qui se trouvent en Gabaa; nous les mettrons à mort, et nous purifierons Israël de ce crime. Mais, les fils de Benjamin ne voulurent point écouter la voix de leurs frères les fils d'Israël.
Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
14 Les fils de Benjamin de toutes les villes se rassemblèrent à Gabaa, pour sortir à la rencontre des fils d'Israël.
Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
15 Et, ce jour-là, les fils de Benjamin, venus de leurs villes, furent recensés au nombre de vingt-trois mille combattants, outre les habitants de Gabaa,
Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
16 Qui furent recensés au nombre de sept cents hommes d'élite, tous ambidextres et frondeurs habiles, lançant des pierres sans s'écarter du but de l'épaisseur d'un cheveu.
Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
17 Et d'Israël, hormis Benjamin, il se trouva quatre cent mille hommes portant l'épée, tous exercé aux combats.
Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
18 Ceux-ci se levèrent, montèrent à Béthel, consultèrent Dieu, et dirent: Qui de nous sera élevé au commandement pour livrer bataille aux fils de Benjamin? Le Seigneur répondit; Juda sera votre chef.
Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
19 Les fils d'Israël se levèrent de grand matin, et ils campèrent devant Gabaa.
Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
20 Et tout Israël sortit du camp pour attaquer Benjamin, et ils en vinrent aux mains avec Gabaa.
Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
21 Les fils de Benjamin sortirent de Gabaa, et détruisirent ce jour-là vingt-deux mille hommes d'Israël.
Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
22 Mais, Israël reprit courage, et il recommença le combat au lieu même où la veille on s'était rencontré.
Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
23 Or, les fils d'Israël étaient montés devant le Seigneur, et ils avaient pleuré jusqu'au soir, et ils avaient consulté le Seigneur, disant: Continuerons-nous d'approcher pour combattre nos frères les fils de Benjamin? Et le Seigneur leur avait répondu: Marchez contre eux.
Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
24 En cette seconde journée les fils d'Israël marchèrent contre les fils de Benjamin;
Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
25 En cette seconde journée, les fils de Benjamin sortirent de Gabaa à leur rencontre, et dix-huit mille des fils d'Israël, tous portant l'épée, périrent encore sur le champ de bataille.
A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
26 Alors, tous les fils d'Israël, tout le peuple, montèrent en Béthel, et ils pleurèrent, et ils s'assirent devant le Seigneur, et ils jeûnèrent tout le jour jusqu'au soir, et ils offrirent en holocauste des victimes sans tache,
Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
27 Devant le Seigneur, car, en ce temps-là, l'arche de l' alliance du Seigneur Dieu était à Béthel;
Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
28 Et Phinées, fils d'Eléazar, fils d'Aaron, en ces jours-là, se tenait devant l'arche. Les fils d'Israël consultèrent donc le Seigneur, disant: Continuerons-nous de sortir pour combattre nos frères les fils de Benjamin? Et le Seigneur leur dit: Partez, demain je vous les livrerai.
Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
29 Et les fils d'Israël dressèrent des embuscades autour de Gabaa,
Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
30 Et les fils d'Israël marchèrent, le troisième jour, contre les fils de Benjamin, et ils en vinrent aux mains, comme les deux autres fois, devant Gabaa.
Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
31 Car les fils de Benjamin marchèrent à la rencontre du peuple; ils sortirent tous de la ville; ils commencèrent à faire tomber des morts dans les rangs du peuple, comme les deux autres fois, sur les chemins qui conduisent l'un à Béthel, l'autre aux champs de Gabaa. Trente hommes environ d'Israël furent atteints.
Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
32 Et les fils de Benjamin dirent: Ils tombent devant nous comme auparavant. Et les fils d'Israël dirent: Fuyons, attirons-les sur les chemins loin de la ville. Ainsi firent-ils.
Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
33 Chacun quitta son poste pour reculer jusqu'à Baal-Thamar; cependant l'embuscade d'Israël survint de Maraagabé, où elle se tenait.
Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
34 Dix mille hommes d'élite, pris parmi tout Israël, arrivèrent en face de Gabaa, et la bataille fut terrible, et les fils de Benjamin ne s'aperçurent pas que le mal fondait sur eux.
Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
35 Et, ce jour-là, le Seigneur frappa Benjamin devant les fils d'Israël, et les fils d'Israël détruisirent de Benjamin vingt-cinq mille cent hommes, tous portant l'épée.
Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
36 Et les fils de Benjamin se virent accablés; car les fils d'Israël leur avaient fait place, comptant sur l'embuscade préparée contre Gabaa.
Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
37 Or, pendant qu'ils avaient reculé, l'embuscade s'était ébranlée, elle s'était déployée autour de la ville, elle s'y était répandue, et elle avait passé tout au fil de l'épée.
Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
38 Les fils d'Israël étaient convenus d'un signal; l'embuscade devait faire monter au-dessus de la ville une colonne de fumée.
Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
39 Les fils d'Israël avaient ainsi reconnu que l'embuscade venait de prendre Gabaa; c'est alors qu'ils avaient engagé la bataille; d'abord Benjamin leur avait tué cent trente hommes, et il avait dit: Les voilà qui tombent encore devant nous comme à la première bataille.
a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
40 Et le signal se montrait plus évident encore au-dessus de la ville, comme une colonne de fumée. Benjamin, ayant regardé derrière lui, vit la ruine de la ville et la fumée s'élevant jusqu'au ciel.
Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
41 C'est alors qu'Israël fit volte-face, et que Benjamin s'enfuit, quand il reconnut que le mal fondait sur lui
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
42 Devant les fils d'Israël; et il tourna les yeux sur le chemin du désert et il prit la fuite; mais le combat l'atteignit, et ceux des autres villes le détruisirent pendant qu'il passait au milieu d'eux.
Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
43 Ils frappèrent Benjamin, ils le poursuivirent, pied à pied, depuis Nua, jusqu'aux monts qui regardent Gabaa du côté de l'orient.
Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
44 La, dix-huit mille hommes de Benjamin périrent, tous dans la force de l'âge.
Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
45 Et les débris de cette armée, regardant autour d'eux, s'enfuirent au désert, du côté du rocher de Rhemmon; mais, chemin faisant, les fils d'Israël en moissonnèrent encore cinq mille; puis, les poursuivant jusqu'à Gedan, ils tuèrent en outre deux mille hommes.
Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
46 Tous ceux de Benjamin qui ce jour-là périrent, montèrent à vingt-cinq mille hommes portant l'épée, tous dans la force de l'âge.
A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
47 Et les débris de cette armée, ayant regardé autour d'eux, s'enfuirent dans le désert vers le rocher de Rhemmon, au nombre de six cents hommes; ils campèrent en ce lieu pendant quatre mois.
Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
48 Et les fils d'Israël parcourant la tribu de Benjamin passèrent tout au fil de l'épée, gens et troupeaux; tout ce qu'ils rencontrèrent périt; et les villes qui se trouvèrent sur leur route furent livrées aux flammes.
Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.

< Juges 20 >