< Proverbes 3 >

1 Mon fils, n'oublie point mes lois, et garde mes paroles en ton cœur;
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 car elles te donneront la longueur des jours, des années de vie, et la paix.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Que la miséricorde et la foi ne te quittent point; mais attache-les à ton cou, et tu trouveras grâce.
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Et pense au bien devant le Seigneur et devant les hommes.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Mets ta confiance en Dieu de tout ton cœur, et ne t'enorgueillis point de ta sagesse.
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 Discerne-la en toutes tes voies, pour marcher droit dans tes sentiers.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Ne te crois point sage par toi-même; mais crains Dieu, et détourne-toi de tout mal.
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Alors la santé sera en ton corps, et le bien-être en tes os.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Rends hommage au Seigneur de tes labeurs prospères, et offre-Lui les prémices des fruits de ta justice.
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 Afin que tes celliers regorgent de froment, et que tes pressoirs débordent de vin.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Mon fils, ne rejette point la discipline du Seigneur; ne te lasse pas d'être réprimandé par Lui.
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 Car le Seigneur reprend celui qu'Il aime, et frappe l'enfant qu'Il préfère.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Heureux l'homme qui a trouvé la Sagesse, et le mortel qui a connu la Prudence.
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Car elle est meilleure à gagner que des trésors entiers d'or et d'argent.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 Elle est plus précieuse que les pierreries; nul mal ne lui résiste; elle est bien connue de tous ceux qui l'approchent; rien de ce qu'on estime n'est digne d'elle.
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 En sa main droite sont les longs jours et les années de vie; en sa gauche, la richesse et la gloire; de sa bouche procède la justice, et sa langue porte la loi et la miséricorde.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Ses voies sont les bonnes voies, et tous ses sentiers pacifiques.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 Elle est l'arbre de vie pour ceux qui l'embrassent; elle est un sûr appui pour ceux qui s'attachent à elle, comme au Seigneur.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Dieu a fondé la terre par la Sagesse; Il a affermi le ciel par la Prudence.
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 Grâce à sa prévoyance, les abîmes ont été rompus, et les nuages ont répandu la rosée.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Mon fils, que ces choses ne s'éloignent pas de toi; garde mes conseils et ma science,
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 afin que ton âme vive, et que la grâce demeure autour de ton cou, la santé sera en ta chair, et le bien-être en tes os;
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 afin que tu marches, en toutes tes voies, plein d'assurance et de paix, et que ton pied ne trébuche pas.
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 Si tu reposes, tu seras sans crainte; si tu sommeilles, tu dormiras doucement.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Tu ne redouteras ni les alarmes soudaines, ni les attaques des impies
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 Car le Seigneur sera sur toutes tes voies, et Il affermira ton pied de peur que tu ne chancelles.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Ne t'abstiens pas de faire du bien à l'indigent, sous prétexte que ta main ne peut le secourir.
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Ne dis pas, quand tu pourras bien faire: Va et reviens, demain je te donnerai; car tu ne sais ce qu'amènera le jour suivant.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Ne pense pas à mal contre ton ami qui vit près de toi, et se fie à toi.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 Ne prends pas en haine un homme sans motif, de peur qu'il ne vienne à te nuire.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Ne t'attire pas les outrages d'hommes méchants; ne porte point envie à leurs voies.
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 Car tout pervers est impur devant le Seigneur, et il ne siégera point dans l'assemblée des justes.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 La malédiction de Dieu est sur la maison des impies; mais les chaumières des justes sont bénies.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 Le Seigneur résiste aux superbes; mais Il donne Sa grâce aux humbles.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Les sages auront la gloire pour héritage; tandis que les impies exalteront leur propre ignominie.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

< Proverbes 3 >