< Sophonie 2 >

1 Rassemblez-vous et priez en commun, ô nation ignorante,
Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
2 avant qu'il soit de vous comme de la fleur qui passe, avant que la colère du Seigneur fonde sur vous, avant que n'arrive sur vous la jour de la colère du Seigneur.
kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
3 Cherchez tous le Seigneur, ô vous humbles de la terre, pratiquez la justice, interrogez l'équité, et répondez-lui, afin d'être abrités au jour de la colère du Seigneur;
Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
4 car Gaza sera pillée, Ascalon sera détruite, Azot tombera en plein midi, et Accaron sera déracinée.
Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
5 Malheur à vous, qui habitez les rivages de la mer, colons des Crétois. La parole du Seigneur est contre vous, Chanaan, terre des Philistins, et Je vous chasserai de vos demeures.
Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
6 Et votre territoire sera un pâturage pour les troupeaux, un parc pour les brebis.
Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
7 Et le rivage de la mer appartiendra aux restes de la maison de Juda; ceux- ci seront nourris dans les demeures d'Ascalon, et ils s'y reposeront le soir, loin de la face des fils de Juda; car le Seigneur leur Dieu les a visité, et Il les fera revenir de la captivité.
Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
8 J'ai entendu les injures de Moab, et les outrages des fils d'Ammon; ils ont insulté Mon peuple, et se sont glorifiés sur Ma terre.
“Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
9 À cause de cela, par Ma vie, dit le Seigneur d'Israël, Dieu des armées, Moab sera comme Sodome, et les fils d'Ammon comme Gomorrhe, et Damas disparaîtra comme le monceau de blé d'une aire, et elle sera effacée pour jamais. Et les restes de Mon peuple les pilleront, et les restes de Ma nation posséderont leur héritage.
Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10 Voilà comment sera punie leur insolence; car en se glorifiant ils ont outragé le Seigneur, Maître de toutes choses.
Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
11 Le Seigneur Se manifestera contre eux, et Il anéantira tous les dieux de la terre et tout homme, en son pays, et toutes les îles des nations finiront par L'adorer.
Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
12 Et vous, Éthiopiens, vous serez aussi blessés de Mon glaive.
“Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
13 Et le Seigneur étendra la main vers l'Aquilon, et Il détruira l'Assyrien, et Il fera de Ninive une ruine sans eau, comme un désert.
Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
14 Et les troupeaux viendront paître au milieu d'elle; et toutes les bêtes fauves de la contrée, et les caméléons, et les hérissons coucheront dans ses palais, et les bêtes farouches hurleront dans ses fossés, et les corbeaux croasseront sur ses portes, elle maintenant aussi altière que le cèdre.
Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
15 Voilà cette ville si méprisante, qui se reposait dans sa confiance et disait en son cœur: J'existe, et il n'est point de ville telle que moi. Comment est-elle devenue une solitude, un repaire de bêtes fauves? Et celui qui passera par là sifflera et battra des mains.
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.

< Sophonie 2 >