< 2 Chroniques 18 >

1 Or Josaphat ayant de grandes richesses et une grande gloire fit alliance avec Achab.
Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
2 Et au bout de quelques années il descendit vers Achab à Samarie, et Achab tua pour lui et pour le peuple qui [était] avec lui un grand nombre de brebis et de bœufs, et le persuada de monter contre Ramoth de Galaad.
Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
3 Car Achab, Roi d'Israël, dit à Josaphat Roi de Juda: Ne viendras-tu pas avec moi contre Ramoth de Galaad? Et il lui [répondit]: Compte sur moi comme sur toi, et sur mon peuple comme sur ton peuple; [nous irons] avec toi à cette guerre.
Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
4 Josaphat dit aussi au Roi d'Israël: Je te prie qu'aujourd'hui tu t'enquières de la parole de l'Eternel.
Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
5 Et le Roi d'Israël assembla quatre cents Prophètes, auxquels il dit: Irons-nous à la guerre contre Ramoth de Galaad, ou m'en désisterai-je? Et ils répondirent: Monte; car Dieu la livrera entre les mains du Roi.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
6 Mais Josaphat dit: N'y a-t-il point encore ici quelque Prophète de l'Eternel, afin que nous l'interrogions?
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
7 Et le Roi d'Israël dit à Josaphat: Il y a encore un homme par lequel on peut s'enquérir de l'Eternel, mais je le hais, parce qu'il ne prophétise rien de bon, quand il est question de moi, mais toujours du mal; c'est Michée fils de Jimla. Et Josaphat dit: Que le Roi ne parle point ainsi.
Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
8 Alors le Roi d'Israël appela un Eunuque, et lui dit: Fais venir en diligence Michée fils de Jimla.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
9 Or le Roi d'Israël et Josaphat Roi de Juda, étaient assis chacun sur son trône, revêtus de leurs habits; ils étaient assis en la place vers l'entrée de la porte de Samarie, et tous les Prophètes prophétisaient en leur présence.
Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
10 Alors Tsidkija fils de Kénahana s'étant fait des cornes de fer, dit: Ainsi a dit l'Eternel, tu heurteras avec ces cornes les Syriens, jusqu'à les détruire entièrement.
To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
11 Et tous les Prophètes prophétisaient la même chose, en disant: Monte à Ramoth de Galaad, et tu prospéreras, et l'Eternel la livrera entre les mains du Roi.
Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
12 Or le messager qui était allé appeler Michée, lui parla, en disant: Voici, les Prophètes prédisent tous d'une voix du bonheur au Roi, je te prie donc que ta parole soit semblable à celle de l'un d'eux, et prophétise-lui du bonheur.
Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
13 Mais Michée répondit: L'Eternel est vivant, que je dirai ce que mon Dieu dira.
Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
14 Il vint donc vers le Roi; et le Roi lui dit: Michée, irons-nous à la guerre contre Ramoth de Galaad, ou m'en désisterai-je? Et il répondit: Montez, et vous prospérerez, et ils seront livrés entre vos mains.
Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
15 Et le Roi lui dit: Jusqu'à combien de fois t'adjurerai-je que tu ne me dises que la vérité au Nom de l'Eternel?
Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
16 Et [Michée] répondit: J'ai vu tout Israël dispersé par les montagnes, comme un troupeau de brebis qui n'a point de pasteur; et l'Eternel a dit: Ceux-ci sont sans Seigneurs; que chacun s'en retourne dans sa maison en paix.
Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
17 Alors le Roi d'Israël dit à Josaphat: Ne t'ai-je pas bien dit qu'il ne prophétise rien de bon, quand il est question de moi, mais du mal?
Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
18 Et [Michée] dit: Ecoutez pourtant la parole de l'Eternel. J'ai vu l'Eternel assis sur son trône, et toute l'armée des cieux se tenant à sa droite et à sa gauche.
Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
19 Et l'Eternel a dit: Qui est-ce qui induira Achab Roi d'Israël à monter, afin qu'il tombe en Ramoth de Galaad? et il ajouta: L'un dit d'une manière, et l'autre d'une autre.
Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
20 Alors un esprit s'avança, et se tint devant l'Eternel, et dit: Je l'y induirai. Et l'Eternel lui dit: Comment?
A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
21 Et il répondit: Je sortirai et je serai un esprit de mensonge en la bouche de tous ses Prophètes. Et [l'Eternel] dit: [Oui] tu l'induiras, et même tu en viendras à bout, sors et fais-le ainsi.
“Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
22 Maintenant donc voici, l'Eternel a mis un esprit de mensonge dans la bouche de tes Prophètes, et l'Eternel a prononcé du mal contre toi.
“To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
23 Alors Tsidkija fils de Kénahana s'approcha, et frappa Michée sur la joue, et lui dit: Par quel chemin l'esprit de l'Eternel s'est-il retiré de moi pour te parler?
Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
24 Et Michée répondit: Voici, tu le verras le jour que tu iras de chambre en chambre pour te cacher.
Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
25 Alors le Roi d'Israël dit: Qu'on prenne Michée, et qu'on le mène à Amon, capitaine de la ville, et vers Joas fils du Roi;
Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
26 Et qu'on leur dise: Ainsi a dit le Roi: Mettez cet homme en prison, et ne lui donnez qu'un peu de pain à manger et un peu d'eau [à boire], jusqu'à ce que je retourne en paix.
ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
27 Et Michée répondit: Si jamais tu retournes en paix, l'Eternel n'aura point parlé par moi. Il dit encore: Entendez cela peuples, vous tous qui êtes ici.
Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
28 Le Roi d'Israël donc monta avec Josaphat Roi de Juda, contre Ramoth de Galaad.
Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
29 Et le Roi d'Israël dit à Josaphat: Que je me déguise, et que j'aille à la bataille; mais toi, vêts-toi de tes habits. Le Roi d'Israël donc se déguisa, et ils allèrent ainsi à la bataille.
Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
30 Or le Roi des Syriens avait commandé aux capitaines de ses chariots, en disant: Vous ne combattrez contre personne que contre le Roi d'Israël.
To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
31 Il arriva donc qu'aussitôt que les capitaines des chariots eurent vu Josaphat, ils dirent: C'est ici le Roi d'Israël; et ils l'environnèrent pour le combattre. Mais Josaphat s'écria, et l'Eternel le secourut; et Dieu les porta à s'éloigner de lui.
Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
32 Or dès que les capitaines des chariots eurent vu que ce n'était point le Roi d'Israël, ils se détournèrent de lui.
gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
33 Alors quelqu'un tira de son arc de toute sa force; et il frappa le Roi d'Israël entre les tassettes et le harnois; et [le Roi] dit à son cocher: Tourne ta main, et mène-moi hors du camp; car on m'a fort blessé.
Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
34 Il y eut en ce jour-là un très rude combat, et le Roi d'Israël demeura dans son chariot, vis-à-vis des Syriens, jusqu'au soir, et il mourut vers le temps que le soleil se couchait.
Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.

< 2 Chroniques 18 >