< 2 Rois 11 >

1 Or Hathalia mère d'Achazia, ayant vu que son fils était mort, s'éleva, et extermina toute la race Royale.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Mais Jéhosébah fille du Roi Joram, sœur d'Achazia prit Joas fils d'Achazia, et le déroba d'entre les fils du Roi qu'on faisait mourir, [et le mit] avec sa nourrice dans la chambre aux lits; et on le cacha de devant Hathalia, de sorte qu'on ne le fit point mourir.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 Et il fut caché avec elle dans la maison de l'Eternel, l'espace de six ans; cependant Hathalia régnait sur le pays.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 Et la septième année Jéhojadah envoya, et prit des centeniers, des capitaines, et des archers, et les fit entrer vers soi dans la maison de l'Eternel, et traita alliance avec eux, et les fit jurer dans la maison de l'Eternel, et leur montra le fils du Roi.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 Puis il leur commanda, en disant: [C'est] ici ce que vous ferez: La troisième partie d'entre vous qui entrez en semaine, fera la garde de la maison du Roi;
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 Et la troisième partie sera à la porte de Sur; et la troisième partie sera à la porte qui est derrière les archers; ainsi vous ferez le guet pour garder le Temple, afin que personne n'y entre par force.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Et les deux compagnies d'entre vous qui sortez de semaine, feront le guet pour garder la maison de l'Eternel, auprès du Roi.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 Et vous environnerez le Roi tout autour, chacun ayant ses armes en sa main, et si quelqu'un entre dans les rangs, qu'il soit mis à mort; vous serez avec le Roi quand il sortira, et quand il entrera.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Les centeniers donc firent comme Jéhojadah le Sacrificateur avait commandé; ils prirent chacun ses gens, tant ceux qui entraient en semaine, que ceux qui sortaient de semaine; et ils vinrent vers le Sacrificateur Jéhojadah.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 Et le sacrificateur donna aux centeniers des hallebardes et des boucliers qui avaient été au Roi David, [et] qui étaient dans la maison de l'Eternel.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 Et les archers se tinrent rangés auprès du Roi tout alentour, ayant chacun les armes à la main, depuis le côté droit du Temple jusqu'au côté gauche, tant pour l'autel que pour le Temple.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Et [Jéhojadah] fit amener le fils du Roi, et mit sur lui la couronne, et le Témoignage, et ils l'établirent Roi, et l'oignirent, et frappant des mains, ils dirent: Vive le Roi!
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Et Hathalia entendant le bruit des archers, et du peuple, entra vers le peuple dans la maison de l'Eternel.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 Et elle regarda, et voilà, le Roi était près de la colonne, selon la coutume des Rois, et les capitaines et les trompettes étaient près du Roi, et tout le peuple du pays éclatait de joie, et on sonnait des trompettes. Alors Hathalia déchira ses vêtements, et cria: Conjuration! conjuration!
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Et le Sacrificateur Jéhojadah commanda aux centeniers qui avaient la charge de l'armée, et leur dit: Menez-la hors des rangs, et que celui qui la suivra soit mis à mort par l'épée; car le Sacrificateur avait dit: Qu'on ne la mette point à mort dans la maison de l'Eternel.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 Ils lui firent donc place; et elle revint dans la maison du Roi par le chemin de l'entrée des chevaux, et elle fut tuée là.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Et Jéhojadah traita alliance entre l'Eternel, le Roi, et le peuple, qu'ils seraient pour peuple à l'Eternel; [il traita] de même [alliance] entre le Roi et le peuple.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Alors tout le peuple du pays entra dans la maison de Bahal, la démolirent, avec ses autels, et ils brisèrent entièrement ses images; ils tuèrent aussi Mattam Sacrificateur de Bahal, devant les autels; et le Sacrificateur ordonna des gardes en la maison de l'Eternel.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 Et il prit les centeniers, les capitaines, les archers, et tout le peuple du pays, et ils firent descendre le Roi de la maison de l'Eternel, et ils entrèrent dans la maison du Roi par le chemin de la porte des archers, et [Joas] s'assit sur le trône des Rois.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 Et tout le peuple du pays fut dans la joie, et la ville fut en repos; quoiqu'on eût mis à mort Hathalia par l'épée dans la maison du Roi.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Joas était âgé de sept ans quand il commença à régner.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Rois 11 >