< 2 Rois 9 >

1 Alors Elisée le Prophète appela un d'entre les fils des Prophètes, et lui dit: Trousse tes reins; et prends cette fiole d'huile en ta main, et t'en va à Ramoth de Galaad.
Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
2 Quand tu y seras entré, regarde où sera Jéhu fils de Josaphat, fils de Nimsi, et y entre, et l'ayant fait lever d'entre ses frères, tu le feras entrer dans quelque chambre secrète.
Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
3 Puis tu prendras la fiole d'huile, tu la verseras sur sa tête, et tu diras: Ainsi a dit l'Eternel: Je t'ai oint pour être Roi sur Israël. Après quoi tu ouvriras la porte, tu t'enfuiras, et tu ne t'arrêteras point.
Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
4 Ainsi ce jeune homme, qui était le serviteur du Prophète, s'en alla à Ramoth de Galaad.
Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
5 Et quand il y fut entré, voici, les capitaines de l'armée étaient là assis; et il dit: Capitaine, j'ai à parler à toi. Et Jéhu répondit: A qui de nous tous parles-tu? Et il dit: A toi, Capitaine.
Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
6 Alors [Jéhu] se leva, et entra dans la maison; [et le jeune homme] lui versa l'huile sur la tête, et lui dit: Ainsi a dit l'Eternel le Dieu d'Israël: Je t'ai oint pour être Roi sur le peuple de l'Eternel; [c'est-à-dire] sur Israël.
Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
7 Et tu frapperas la maison d'Achab ton Seigneur; car je ferai vengeance du sang de mes serviteurs les Prophètes, et du sang de tous les serviteurs de l'Eternel, [en le redemandant] de la main d'Izebel.
Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
8 Et toute la maison d'Achab périra, et je retrancherai à Achab depuis l'homme jusqu'à un chien, tant ce qui est serré que ce qui est délaissé en Israël.
Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
9 Et je mettrai la maison d'Achab au même état que la maison de Jéroboam fils de Nébat, et la maison de Bahasa, fils d'Ahija.
Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
10 Les chiens aussi mangeront Izebel au champ de Jizréhel, et il n'y aura personne qui l'ensevelisse; après quoi il ouvrit la porte, et s'enfuit.
Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
11 Alors Jéhu sortit vers les serviteurs de son maître, et on lui dit: Tout va-t-il bien? Pourquoi cet insensé est-il venu vers toi? Et il leur répondit: Vous connaissez l'homme, et ce qu'il sait dire.
Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
12 Mais ils dirent: Ce n'est pas cela; déclare nous-le maintenant. Et il répondit: Il m'a dit telle et telle chose; il m'a dit: Ainsi a dit l'Eternel, je t'ai oint pour être Roi sur Israël.
Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
13 Alors ils se hâtèrent, et prirent chacun leurs vêtements, et les mirent sous lui au plus haut des degrés, et sonnèrent de la trompette, et dirent: Jéhu a été fait Roi.
Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
14 Ainsi Jéhu fils de Josaphat, fils de Nimsi se ligua contre Joram. Or Joram avait muni Ramoth de Galaad, lui et tout Israël, de peur d'Hazaël Roi de Syrie.
Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
15 Et le Roi Joram s'en était retourné pour se faire panser à Jizréhel des plaies que les Syriens lui avaient faites, quand il combattit contre Hazaël Roi de Syrie. Et Jéhu dit: Si vous le trouvez bon, [empêchons] que personne ne sorte ni n'échappe de la ville pour aller porter [cette nouvelle] à Jizréhel.
amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
16 Alors Jéhu monta à cheval, et s'en alla à Jizréhel, car Joram était là malade; et Achazia Roi de Juda y était descendu pour visiter Joram.
Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
17 Or il y avait une sentinelle sur une tour à Jizréhel, qui voyant venir la troupe de Jéhu dit: Je vois une troupe de gens. Et Joram dit: Prends un homme de cheval, et l'envoie au-devant d'eux, et qu'il dise: Y a-t-il paix?
Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
18 Et l'homme de cheval s'en alla au-devant de lui, et dit: Ainsi dit le Roi: Y a-t-il paix? Et Jéhu répondit: Qu'as-tu à faire de paix? Mets-toi derrière moi; et la sentinelle le rapporta, en disant: Le messager est venu jusqu'à eux, et il ne retourne point.
Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
19 Et il envoya un autre homme de cheval, qui vint à eux, et dit: Ainsi a dit le Roi: Y a-t-il paix? Et Jéhu répondit: Qu'as-tu à faire de paix? Mets-toi derrière moi.
Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
20 Et la sentinelle le rapporta, et dit: Il est venu jusqu'à eux, et il ne retourne point; mais la démarche est comme la démarche de Jéhu fils de Nimsi; car il marche avec furie.
Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
21 Alors Joram dit: Qu'on attelle; et on attela son chariot. Ainsi Joram Roi d'Israël sortit avec Achazia Roi de Juda, chacun dans son chariot, et ils allèrent pour rencontrer Jéhu, et ils le trouvèrent dans le champ de Naboth Jizréhélite.
Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
22 Et dès que Joram eut vu Jéhu, il dit: N'y a-t-il pas paix, Jéhu? Et [Jéhu] répondit: Quelle paix, tandis que les paillardises de ta mère Izebel, et ses enchantements seront en si grand nombre?
Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
23 Alors Joram tourna sa main, et s'enfuit; et dit à Achazia: Achazia, nous sommes trompés.
Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
24 Et Jéhu empoigna l'arc à pleine main, et frappa Joram entre ses épaules, de sorte que la flèche sortait au travers de son cœur, et il tomba sur ses genoux dans son chariot.
Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
25 Et [Jéhu] dit à Bidkar son capitaine: Prends[-le, et] le jette en quelque endroit du champ de Naboth Jizréhélite; car souviens-toi que quand nous étions à cheval moi et toi, l'un près de l'autre, à la suite d'Achab son père, l'Eternel prononça cette charge contre lui;
Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
26 Si je ne vis hier au soir le sang de Naboth, et le sang de ses fils, dit l'Eternel, et si je ne te le rends dans ce champ-ci, dit l'Eternel; c'est pourquoi prends[-le] maintenant et le jette dans ce champ, suivant la parole de l'Eternel.
‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
27 Or Achazia Roi de Juda ayant vu cela, s'était enfui par le chemin de la maison du jardin; mais Jéhu l'avait poursuivi, et avait dit: Frappez aussi celui-ci sur le chariot. Ce fut dans la montée de Gur qui est auprès de Jibleham; puis il s'enfuit à Meguiddo, et mourut là.
Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
28 Et ses serviteurs l'emmenèrent sur un chariot à Jérusalem, et l'ensevelirent dans son sépulcre avec ses pères, en la Cité de David.
Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
29 Or l'onzième année de Joram fils d'Achab, Achazia avait commencé à régner sur Juda.
(A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
30 Et Jéhu vint à Jizréhel, et Izebel ayant appris [que Jéhu venait], farda son visage, orna sa tête, et elle regardait par la fenêtre.
Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
31 Et comme Jéhu entrait dans la porte, elle dit: En a-t-il bien pris à Zimri qui tua son Seigneur?
Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
32 Et il leva sa tête vers la fenêtre, et dit: Qui est ici de mes gens? Qui? Alors deux ou trois des Eunuques regardèrent vers lui.
Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
33 Et il leur dit: Jetez-la en bas. Et ils la jetèrent, de sorte qu'il rejaillit de son sang contre la muraille, et contre les chevaux, et il la foula aux pieds.
Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
34 Et étant entré, il mangea, et but; puis il dit: Allez voir maintenant cette maudite-là, et l'ensevelissez, car elle est fille de Roi.
Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
35 Ils s'en allèrent donc pour l'ensevelir; mais ils n'y trouvèrent rien que le crâne, et les pieds, et les paumes des mains.
Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
36 Et étant retournés ils le lui rapportèrent; et il dit: C'est la parole de l'Eternel laquelle il avait proférée par le moyen de son serviteur Elie Tisbite, en disant: Dans le champ de Jizréhel les chiens mangeront la chair d'Izebel.
Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
37 Et la charogne d'Izebel sera comme du fumier sur le dessus du champ dans le champ de Jizréhel; de sorte qu'on ne pourra point dire: C'est ici Izebel.
Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”

< 2 Rois 9 >