< 2 Samuel 23 >

1 Or ce sont ici les dernières paroles de David. David fils d'Isaï, l'homme qui a été élevé, pour être l'Oint du Dieu de Jacob, et qui compose les doux cantiques d'Israël, dit:
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
2 L'Esprit de l'Eternel a parlé par moi, et sa parole a été sur ma langue.
“Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
3 Le Dieu d'Israël a dit, le Rocher d'Israël m'a parlé, [en disant]: Le juste dominateur des hommes, le dominateur en la crainte de Dieu,
Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
4 Est comme la lumière du matin quand le soleil se lève, du matin, [dis-je], qui est sans nuages; [il est comme] l'herbe qui sort de la [terre] après la lumière [du soleil] quand il [paraît] après la pluie.
yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
5 Mais il n'en sera pas ainsi de ma maison envers le [Dieu] Fort, parce qu'il a traité avec moi une alliance éternelle bien établie, et assurée; car [c'est] tout mon salut, et tout mon plaisir; c'est pourquoi il ne fera pas [simplement] germer [ma maison].
“Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
6 Mais les méchants seront tous ensemble comme des épines qu'on jette au loin, parce qu'on ne les prend point avec la main.
Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
7 Mais celui qui les veut manier, prend [ou] du fer, ou le bois d'une hallebarde; et on les brûle entièrement sur le lieu même.
Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
8 Ce sont ici les noms des vaillants hommes que David avait: Joseb-Basebeth Tachkémonite était un des principaux capitaines; c'était Hadino le Hetsnite, qui eut le dessus sur huit cents hommes qu'il tua en une seule fois.
Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
9 Après lui était Eléazar, fils de Dodo, fils d'Ahohi, [l'un de ces] trois vaillants hommes qui étaient avec David lorsqu'on rendit honteux les Philistins assemblés là pour combattre, et que ceux d'Israël se retirèrent.
Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
10 Il se leva, et battit les Philistins, jusqu'à ce que sa main en fut lasse, et qu'elle demeura attachée à l'épée; en ce jour-là l'Eternel accorda une grande délivrance, et le peuple retourna après Eléazar, seulement pour prendre la dépouille.
amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
11 Après lui [était] Samma fils d'Agné Hararite; car les Philistins s'étant assemblés dans un bourg où il y avait un endroit d'un champ plein de lentilles, et le peuple fuyant devant les Philistins;
Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
12 Il se tint au milieu de cet endroit du champ, et le défendit, et frappa les Philistins; tellement que l'Eternel accorda une grande délivrance.
Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
13 Il en descendit encore trois d'entre les trente capitaines qui vinrent au temps de la moisson vers David, dans la caverne d'Hadullam, lorsqu'une compagnie de Philistins était campée en la vallée des Réphaïms.
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
14 David était alors dans la forteresse, et la garnison des Philistins était en ce même temps-là à Bethléhem.
Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
15 Et David fit ce souhait, et dit: Qui est-ce qui me ferait boire de l'eau du puits qui est à la porte de Bethléhem?
Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
16 Alors ces trois vaillants hommes passèrent au travers du camp des Philistins, et puisèrent de l'eau du puits qui est à la porte de Bethléhem, et l'ayant apportée, ils la présentèrent à David, lequel n'en voulut point boire, mais il la répandit en présence de l'Eternel.
Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
17 Car il dit: Qu'il ne m'arrive jamais, ô Eternel! de faire une telle chose. N'est-ce pas là le sang de ces hommes qui ont fait ce voyage au péril de leur vie? Il n'en voulut donc point boire. Ces trois vaillants [hommes] firent cette action-là.
Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
18 Il y avait aussi Abisaï frère de Joab fils de Tséruja, qui [était] un des principaux capitaines; celui-ci lançant sa hallebarde contre trois cents hommes, les blessa à mort, et il s'acquit un grand nom entre les trois.
Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
19 Ne fut-il pas le plus estimé entre ces trois-là? c'est pourquoi aussi il fut leur chef; cependant il n égala point les trois premiers.
Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
20 Bénaja aussi fils de Jéhojadah, fils d'un vaillant homme, de Kabtléël, avait fait de grands exploits. Il frappa deux des plus puissants hommes de Moab; il descendit aussi et frappa un lion dans une fosse en un jour de neige.
Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
21 Il frappa aussi un homme Egyptien, [qui était] un bel homme. Cet Egyptien avait en sa main une hallebarde; mais Bénaja descendit contre lui avec un bâton, arracha la hallebarde de la main de l'Egyptien, et le tua de sa propre hallebarde.
Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
22 Bénaja fils de Jéhojadah fit ces choses-là, et fut illustre entre les trois vaillants hommes.
Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
23 Et fut plus honoré que les trente; encore qu'il n'égalât point ces trois-là: c'est pourquoi David l'établit sur ses gens de commandement.
Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
24 Hasaël, frère de Joab, était des trente; Elhanan fils de Dodo, de Bethléhem;
Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
25 Samma Harodite; Elika Harodite;
Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
26 Helets Paltite; Hira fils de Hikkes, Tékohite;
Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
27 Abihézer Hanathothite; Mebunnai Husathite;
Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
28 Tsalmon Ahohite; Maharaï Nétophathite;
Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
29 Héleb fils de Bahana Nétophathite; Ittaï fils de Ribaï de Guibha des enfants de Benjamin;
Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
30 Bénaja Pirhathonite; Hiddaï des vallées de Gahas;
Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
31 Abi Halbon Harbathite; Hazmaveth Barhumite;
Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
32 Eliachba Sahalbonite; [des] enfants de Jesen, Jonathan;
Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
33 Samma Hararite; Ahiam fils de Sarar Hararite;
ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
34 Eliphélet, fils d'Ahasbaï, fils de Mahacati; Eliham fils d'Achithophel Guilonite;
Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
35 Hetseraï Carmélite; Parahaï Arbite;
Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
36 Jiguéal fils de Nathan de Tsoba; Bani Gadite;
Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
37 Tsélek Hammonite; Naharaï Béérothite, qui portait les armes de Joab fils de Tséruja;
Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
38 Hira Jithrite; Gareb Jithrite;
Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
39 Urie Héthien; en tout trente-sept.
da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.

< 2 Samuel 23 >