< Exode 10 >

1 Et l'Eternel dit à Moïse: va vers Pharaon, car j'ai endurci son cœur, et le cœur de ses serviteurs, afin que je mette au-dedans de lui les signes que je m'en vais faire.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 Et afin que tu racontes, ton fils et le fils de ton fils l'entendant, ce que j'aurai fait en Egypte, et mes signes que j'aurai faits entre eux; et vous saurez que je [suis] l'Eternel.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Moïse donc et Aaron vinrent vers Pharaon, et lui dirent: ainsi a dit l'Eternel le Dieu des Hébreux: jusques à quand refuseras-tu de t'humilier devant ma face? Laisse aller mon peuple afin qu'ils me servent.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Car si tu refuses de laisser aller mon peuple, voici, je m'en vais faire venir demain des sauterelles en tes contrées
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Qui couvriront toute la face de la terre, tellement qu'on ne pourra voir la terre: et qui brouteront le reste de ce qui est échappé, que la grêle vous a laissé; et brouteront tous les arbres qui poussent dans les champs.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Et elles rempliront tes maisons, et les maisons de tous tes serviteurs; et les maisons de tous les Egyptiens; ce que tes pères n'ont point vu, ni les pères de tes pères, depuis le jour qu'ils ont été sur la terre, jusqu'à aujourd'hui. Puis ayant tourné le dos à Pharaon, il sortit d'auprès de lui.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Et les serviteurs de Pharaon lui dirent: jusques à quand celui-ci nous tiendra-t-il enlacés? Laisse aller ces gens, et qu'ils servent l'Eternel leur Dieu. [Attendras-]tu de savoir avant cela que l'Egypte est perdue?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Alors on fit revenir Moïse et Aaron vers Pharaon; et il leur dit: allez, servez l'Eternel votre Dieu. Qui sont tous ceux qui iront?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Et Moïse répondit: nous irons avec nos jeunes gens et nos vieillards, avec nos fils et nos filles, avec notre menu et gros bétail; car nous avons [à célébrer] une fête solennelle à l'Eternel.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Alors il leur dit: que l'Eternel soit avec vous, comme je laisserai aller vos petits enfants; prenez garde, car le mal est devant vous.
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Il n'en sera [donc] pas ainsi [que vous l'avez demandé], mais vous hommes, allez maintenant, et servez l'Eternel; car c'est ce que vous demandez. Et on les chassa de devant Pharaon.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Alors l'Eternel dit à Moïse: étends ta main sur le pays d'Egypte [pour faire] venir les sauterelles, afin qu'elles montent sur le pays d'Egypte, et qu'elles broutent toute l'herbe de la terre, et tout ce que la grêle a laissé de reste.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Moïse donc étendit sa verge sur le pays d'Egypte, et l'Eternel amena sur la terre un vent Oriental tout ce jour-là et toute la nuit; [et] au matin le vent Oriental eut enlevé les sauterelles.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Et il fit monter les sauterelles sur tout le pays d'Egypte, et les mit dans toutes les contrées d'Egypte, elles étaient fort grosses, et il n'y en avait point eu de semblables avant elles, et il n'y en aura point de semblables après elles.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 Et elles couvrirent la face de tout le pays, tellement que la terre en fut couverte; et elles broutèrent toute l'herbe de la terre, et tout le fruit des arbres que la grêle avait laissé, et il ne demeura aucune verdure aux arbres, ni aux herbes des champs, dans tout le pays d'Egypte.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Alors Pharaon fit appeler en toute diligence Moïse et Aaron, et [leur] dit: j'ai péché contre l'Eternel votre Dieu, et contre vous.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Mais maintenant, je te prie, pardonne-moi mon péché, seulement pour cette fois; et fléchissez l'Eternel votre Dieu par prières, afin qu'il retire de moi cette mort-ci seulement.
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Il sortit donc d'auprès de Pharaon, et il fléchit l'Eternel par prières.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Et l'Eternel fit lever à l'opposite un vent très-fort de l'Occident, qui enleva les sauterelles, et les enfonça dans la mer rouge. Il ne resta pas une seule sauterelle dans toutes les contrées d'Egypte.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Mais l'Eternel endurcit le cœur de Pharaon, et il ne laissa point aller les enfants d'Israël.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Puis l'Eternel dit à Moïse: Etends ta main vers les cieux, et qu'il y ait sur le pays d'Egypte des ténèbres [si épaisses], qu'on les puisse toucher à la main.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Moïse donc étendit sa main vers les cieux; et il y eut des ténèbres fort obscures en tout le pays d'Egypte durant trois jours.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 L'on ne se voyait pas l'un l'autre, et nul ne se leva du lieu où il était pendant trois jours; mais il y eut de la lumière pour les enfants d'Israël dans le lieu de leurs demeures.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Alors Pharaon appela Moïse, et lui dit: allez, servez l'Eternel; seulement que votre menu et gros bétail demeurent; même vos petits enfants iront avec vous.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Mais Moïse répondit: tu nous laisseras aussi amener les sacrifices et les holocaustes que nous ferons à l'Eternel notre Dieu.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 Et même nos troupeaux viendront avec nous, sans qu'il en demeure un ongle; car nous en prendrons pour servir à l'Eternel notre Dieu; et nous ne savons pas ce que nous offrirons à l'Eternel, jusques à ce que nous soyons parvenus en ce lieu-là.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Mais l'Eternel endurcit le cœur de Pharaon, et il ne voulut point les laisser aller.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Et Pharaon lui dit: va-t'en arrière de moi; donne-toi de garde de voir plus ma face; car au jour où tu verras ma face, tu mourras.
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Et Moïse répondit: tu as bien dit; je ne verrai plus ta face.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< Exode 10 >